Showing 255001 words to 258000 words out of 495987 words
Chapter 86 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
rungume belt din na sauka ajikinsu "kunga bala'in da musa ya jawo min kou ina zaman zamana ? dole ne ya rabu musu da yarinya mana nifa na gaji da wannan wahalar ta karasa maganar tana rushewa da kuka tana kokarin kamo Aliyu kafafuwan Aliyu amman ina sake tureta yayi yana haci tamkar kumurcin maciji .."
mumy kuwa tuni numfashinta ya soma barazanar daukewa ya badamasi dake kanta ya dinga kokarin numfashinta ya daidaita sai dai har lokacin numfashin yaki daidai sai haki take tana huci kwayar idanunta nayin sama a matukar fusace muradi yace "waye stupid goat din dake damun rayuwar sister dina who's that animal ? ya tambaya a tsawace yana kaiwa bango nashi dan shi ko a hanya ya ga musa zai wuce ya wuce dan bai sanshi ba Zainab tace "ga dan iskan can kaci ubansa ya Ali "what wannan dan yaron ? Zainab ta gyada masa kai "wannan snal din take so ? yayi magana yana kallon Musa tare da nuna shi da yatsa ..."
Take Musa ya shiga girgiza masa dan ya bala'in tsorata da ganin yanayin Aliyu dan a yadda yake kallonsa zai iya kashe mutun har lahira sosai Aliyu ya daura idanunshi akan Musa dake rike da hannunsa daya karye , ganin irin kallon da Aliyu ke masa yasa musa soma ja da baya domin guduwa shi kuwa baban musa tuni ya lalla'ba ya shige daki ya kulle kofarsa tun kafin Aliyu ya gama da musa ya dawo kanshi dan ya lura babu wanda Aliyu bai doka ba a gidan ."
Aliyu na gama kallon Musa yasa ƙafarsa daya yayi wani irin kwallo dashi Musa yayi sama ya zube kasa yana haki kamar ransa zai fita "kai ! kai !! kai!!! ne kake dagulawa iyayenmu lisafi ?" ya dinga kwallo da musa yana takashi take gidan ya kaure da ihu neman taimakon za'a yi kisan kai kusan yoroba da ihun akan faɗa idan abu yayi bala'in , gida ya sake cika makil da mutane yan bada hakuri yayinda wasu daga cikin mutanen dake tsaye agurin suka fara magana "amman wannan soja ne dai ko kalli yadda yaki dukansu kamar ya samu dabbobi ,wanda ke tsaye kusa dashi yace "wallahi yayi min daidai Allah yasa yayi masa laga laga shegen yaro mai nacin tsiya yana neman bata rayuwar yarinya .
kisna kuwa da iyakacin karfinta take buga kofar tana kiran sunan musa hawaye na bin kuncinta ,cikin dacin rai haɗe da bakinciki Aliyu ya kai kafarshi ya daki kofar dakin duka daya sai ga kofar ta balle kisna ta fito a gigice idanunta bai kai ga kowa ba sai kan musa Wanda ke kwance baya motsi , da gudu ta karasa gurinsa ta zube bisa gwiwowinta ta kife kanta a jikinsa taji baya motsi nan ta soma jijiga shi tana kuka tana kiran sunansa kuka take sosai mai matukar cin rai "waye ya masa haka ?
"Bolaji tace wannan yayan naki ne "ta bata amsa tana kukan zugin belt din Aliyu , kisna ta d'ago idanunta ta kalli wanda aka nuna mata Aliyu ta gani idanunta na tsiyayar da ruwan hawaye sam idanunta sun rufe ko inda mumy take bata kalla ba ta mike da sauri ta ɗauke Aliyu da mari Wanda yasa take numfashin mumy ya dauke ta daina numfashi gabadaya , yayinda zuciyar Samir da madu da ya badamasi suka tsaya cak suka daina aiki na wani lokaci kafin daga baya zuciyoyinsu ya soma bugawa da karfi hatta zuciyar afra ta kusan tarwatsewa saboda tsananin tashin hankali da firgici abinda kisna tayi , abu kamar a mafarki wai kisna ta mari Aliyu akan Musa ? sam firgicin marin da kisna tayiwa Aliyu bai sa sun lura da daukewar numfashin mumy ba . "me yasa ka dokesa har ya daina motsi zaka kashesa ne ? " ni ya kamata Ku kashe tunda bakwa soma bashi ba , "me ya maka da zaka kashesa ? ta sake daga hannu zata sauke masa wani marin Samir yayi saurin mikewa ya rike hannunta ya soma gaugaura mata mari hagu da dama , ta fixge hannuwanta tana kuka "wallahi kun damu rayuwata ku kyaleni mana dole sai kun hanani soyayya da Musa ,ni musa nake so bazan taba rayuwa babu shi ba kuma babu wanda zan aura sai Musa ......"
Tunda kisna ta mari aliyu yayi mutuwar tsaye yana dubanta q'irjinsa na wani irin bugawa da matsanancin karfin gaske , a zahiri ake iya kallon yadda zuciyarsa ke tafasa , jijiyon kasa gabad'aya sun yi rudu rudu , Kallonta kawai yake zuciyarsa na mamakinta , bai bata expecting zata iya kai hannuta jikinsa ba ,duka guda nawa kisna take yarinyar da loma daya zai yi daita ya gama da ita amman ta Iya karfin halin marin mutun irinsa ?
gabad'aya jikinsa yayi sanyi karfinsa yayi kasa yaji kamar zuciyarsa zata buga wani irin bakinciki ne daskare da zuciyarsa yana jin kamar ya zube kasa saboda sanyi da kafafunsa sukayi , yan uwan musa kuwa babu Wanda bai ji dadin marin da kisna tayi wa Aliyu ba Samir ya sake dauketa da wani marin sannan ya shiga dukanta yana kwallo daita madu ya samu sanda ya dinga maka mata tana ihu "zasu kasheni wayyo zasu kasheni shi kam Aliyu ya kasa hanasu dukanta yayi shiru kawai saboda zuciyar dake zafi .
zainba ce ta lura da mumy bata numfashi tasa ihu "mumy bata nufashi fa ku rabu da kisna take suka yo Kan mumy suna rige rige har Aliyu shi kadai ya dauki mumy ya fito waje daita sai lokacin hawaye ya zubo masa har akan fuskar mumy kai tsaye gurin mota ya nufa ya badamasi da Samir suka sa hannu suka saka mumy a bayan mota Zainab da afra suka zagaya suka shiga Aliyu ya shiga mazaunin direba cikin zafin nama hawaye na gangaro masa ya juya motar madu da samir na rike da hannu kisna dake kuka suka bar unguwar ,Aliyu ya kalli ya badamasi ta mirrow ina muka nufa da mumy ?"Muje gida a kofar gida suka iske dady goye da hannuwansa duka a baya zuciyarsa na zafi dan mai gadi ya sheida masa abinda ya faru kamar yadda ya sheidawa Aliyu ganin ana ƙoƙarin fito da mumy gabansa yayi mummunar faduwa ya saki hannunsa yayi gurin motar yana tambayarsa "me ya faru babu wanda ya yi bashi amsa saboda gabad'aya a rud'e suke suka shiga cikin gida ya badamasi ya nufi bangaren sa cikin sauri domin dauko kayan aikinsa tare da Afra suka dawo ya shiga bawa mumy taimakon gaugauwa cikin haka Samir suka shigo da kisna ai kuwa dady yayi kukan kura yayi kanta ya dinga dukanta "zaki kashe uwarki ko ? "Kina son ta mutu ko ?
"A'a dady ku kyaleni karku kasheni wallahi bazan sake fita ba na tuba ku kyaleni "karya kike kullum haka kike faɗa kai madu dauko min sansar can na karya kafar fita da sauri madu ya dauko dady ya dinga makasa kakafuwanta sanda Afra ta dinga bawa dady hakuri tana kuka Zainab t cikin kuka ta karaso ta dungure mata kai "bakya jin magana kisna kina son kashe mumy daga zubar da shafa kika sa kafa kika fita wallahi dady ko Musa nada laifi laifin kisna yafi yawo tunda ita na waya gareta ba idan bataje gurinsa ba bashi da hanyar da zai nemeta "ai yau sai na balla kafar fita nemansa tun kisna na ihu ana iya jinta har aka zo ba'a jin muryarta yayinda Aliyu ke zaune yana Kallonsu ya kasa dakatar dady gashi kukan da yake yasa ya badamasi dake dakin mumy domin ƙoƙarin dawo da numfashinta yace fito da kyar ya samu ya dawo daidai sai dai bata buɗe idanunta ba ya daura mata drip ya fito tana kallon kisna dake nad'e shi ya ma rasa abinda zai mata dan idan yace zai taba kasheta zai yi bayan dady da Samir sun mata lilis sun tabbatar da bazata iya daga kafafunta ba suka kyaleta "kwanto min igiyar shan madu da sauri ya yaje ya kwanto ya dawo "ku daure mata ita kafin gobe na daba mari wallahi dana rasa salaha akanki gara ki damgwama a kulle shasha dabba damsulbasee ,ban da ke kidahumace ma zaki yi da wannan da bai da mutunci yaron da ko ganina yayi sai dai ta daga min kafada saboda kin bashi damar ta raina mu yana tsaye aka daureta yayinda Aliyu da Afra har da zainab ke kuka "dan Allah karku daureta dady ku bata last chance bazata sake ba inji cewar Afra ko saurararta bai ba ana gama daure kisna aka jefe ta bq aka kulle ranar kwana suka yi akan mumy sai cikin dare ta farka da sunan kisna Aliyu ya rikota yana mata sannu dady ya talla'bo Kanta ya bata ruwa tasha tana cewa "kisna ?
"Ki kwantar da hankali mumy bamu barta tana gida "muje ku kaini na ganta "salaha kinsan ba baza yi miki karya ba tana bq daga yau matsalarmu ta kare ki kwantar da hankali gobe da yarda Allah mari zan sa mata wasu hawaye masu zafi suka zubo mata Aliyu ya tare "kiyi hakuri mumy ki daina zubar mata da hawaye maseefa ne a gareta kiyi mata addu'a zata daina ta jijina masa kawai zainab ta shigo da plet din abinci Samir ya amsa ,shima ya Aliyu ya amsa a hannusa ya soma ƙoƙarin bawa mumy "bazan iya cin komai ba muradi yau ni aka watsawa kalanzir har ana neman a shana irin wannan zaka dauki d'anka ka bashi takarashe maganar tana kuka har washegari kuma mumy take wanda hakan yasa jinita ya hau ya wuce ka'ida yayinda zuciyarta ta dinga mata ciwo ko mikewa bata iyayi gabad'aya ciwon mumy yasa aka manta da kisna har bayan kwana biyu mumy dubesu gabad'ayansu harssu zahra da mufeeda da aunty ummi suna zaune a gabanta banda kisna ,tace "kun manta da kisna ko ?
Sukayi shiru cike da takaici a"kuyi hakuri ku duota karta ,kuyi hakuri nasan zan mutu na barku da aiki kuyi iya yinku ko bayan raina ban yarda ku bar kisna ta auri wannan yaron ba duk suka gyada mata "inshallahu mumy ai idan muka bari sunyi galaba akanki ki kwantar da hankalinki bazamu taba yarda ba inji cewar madu duk hirar da'ake hankalin mumy na gurin kisna lura da hakan da Aliyu yayi ya tashi ya shiga Kitchen ya zuba abinci a plet ya dauko goron ruwan ya nufi dakin tana nan a daure,duk kafafuwanta sun kunbura haka fuskantar duk sun kun bura ya durkusa a gabanta ya ajiye plet din abinci ya soma ƙoƙarin kwance ta, ta zuba masa ido tana kallonsa har ya gama batace masa kalla ba haka shima bai ce mata ba ya kai spoon din abinci bakinta saboda yasan bazata iya daga hannunta ba sai dai juyin duniya taki ci ta soma motsi da bakinta yayi kokarin fuskantarta domin jin abinda zata ce a hankali ya fahimci abinda take fada "me yasa ka kwanceni gara ku barni na mutu nafi son mutuwa da rayuwar duniya ".
Ya kura mata ido yana kallon karamin bakinta "lallai wannan yarinyar tana da mugun taurin kai ga kafuwar zuciya kamar ta arna tunda ta fadi abinda ke ranta ta kife kanta
Hannunshi daya ya kai kan suman kanta dake zube har gadon bayanta yana shafawa a hankali yana tunanin kalar rarrashin da zai mata wanda zai natsar da zuciya , wani irin tausayinta yake ji yana ratsa jinin jikinsa , zuciyarsa ke kwabarsa akanta sai dai har lokacin matsayinta na nan na diyar mumynsa shi yasan da wata ce tayi masa abinda tayi masa da ya kulle daita har duniya ta nade amman ita din dabam ce hannunsa ya cigaba da yawo dashi akanta kafin daga baya ya fara magana cikin sanyi murya "ya kamata zuwa yanzu kiyi tunani mai kyau duk dai har yanzu akwai kuruciya acikin lamarinki ,wannan yaron mai kama da tana sam bai dace da mace irinki ba me yasa bazai canza tunaninki ba ya dawo irin namu dan ...."A fusace ta katseshi tana buge masa hannunsa dake kanta sannan ta zuba masa idanunta muryata a shake tace " tunanina ba irin naku bane kuma bazai taɓa dawowa irin naku ba saboda haka har abada bazan taba daina son Musa ba " ya tsareta da kyawawan idanunsa da suka dawo jajayen tsabar damuwa "ka fita a dakina bana kaunar ganinka saboda na tsaneka na tsaneka i really hate you tayi maganar tana kuka " ya watsa mata wani kallo wanda ya tabbatar masa da wasu abubuwa tsakaninta da Allah ta tsaneshi kamar yadda ta fada tsana kuma bata wasa amman shi bai taba jin zai tsaneta ba ko dan darajan mumy ita din uwa ce ta dabam a zuciyarsa komai yana yi ne darajan mumy da sunan Hajiya kayi if not ko kallon arziki bai kamata yayi mata ba bare tausayawa, a hankali ya mike ya bar daki zuciyarsa cike da wasi wasi tunda ya fita ta kife kanta take kuka bata d'ago ba har bacci yayi awon gaba daita...
Mumy da Aliyu sai da suka kai ruwa rana da dady aka sakawa kisna mari kuka suke suna rokonsa karya sa mata mari maganar har gurin hajiya Aysha sai data tako da kanta sannan dady ya hakura sai dai yace bata sake fita babu zuwa boko babu zuwa islamiyya ta zauna anan muddin rai Hajiya Aysha tace "hukuncinka yayi daidai jairar yarinyar so take taga bayanku da ikon Allah sai Allah ya kunyatata bari naje na ga mara jin magana suka tashi tare da aunty Afra dady ya basu key tana zaune ta d'aura kanta akan gwiwowinta kamar koda yaushe ta bushe ta rami tayi wani irin baki tamkar ba kisna ba saboda rashin cin abinci da kulawa dan yadda aka kawo mata abinci haka ake zuwa a tadashi ,aunty Afra na d'aura idanunta akanta ta k'arasa da sauri ta durkusa a gabanta ta rungumeta "baby nah ......"
Kisna ta runtse idanunta gam dan bata qaunar ganin kowa daga cikin ahlinta hajiya Aysha tace" sannu shugaban marasa jin magana Allah dai yasa kiji magana yarinya kamar mai kunne kashi ,ina ke ina jikan oduduwa masu fitsari a tsaye ? " duk da cikin yoroba muka taso amman me zamuyi dasu wallahi kikayi kuskuren da kika gurbata min zuri'a bazan taba yafe miki ba ,ke yanzu rayuwar yayyenki da kika taso kika gani a gidan nan bai isheki misali ba ? "gabadayansu babu wanda yayi saurayin kansa sai wanda aka zaba musu amman ke dan rashin jin kece sai dan gurguwa aunty afra ta d'ago tana duban hajiya Aysha fuskarta da alamar tambaya "daman mahaifiyar yaron gurguwa ce ? "Ke da kukaje gidan baki ga alama ba "Ai bata da maraba da gurguwa baki ga kafafunta ba hagu a dama ba ai sai da aka kwantata min ita sosai sannan na ganeta na san kakar yaron wacce ta haifi ubansa gabad'aya daginsu marasa mutunci ne acikin yoroba , Allah dai ya shiiryeki sakina yasa ki gane daga faɗa Hajiya ta dawo yi mata addu'a akan Allah yaye mata abinda ke damunta anan ta tafi ta bar aunty Afra rungume da kisna dake kuka a tun sanda Hajiya ta soma zaginta ..."
Aunty afra ta kira sunanta cikin sanyi murya "kisna ina son tambayarki wani abu kuma ina bukatar ki faɗa min gaskiya kun taɓa zuwa wani guri da musa kunyi imole ne ma'ana (cin maganin soyayya ) ?Ta girgiza mata kai alamun a'a " ki faɗa min gskiya idan kun taba zuwa sai an san yadda za'a yi a karya kin san dai babu wanda zan fadawa wannan maganar "Allah aunty Afra bamu taɓa yi ba mun dai taba zuwa gurin wani malami amman shi cewa yayi zamuyi aure amman sai mumy ta mutu "ya rabbi yanzu ke zaki auri wanda sai mahaifiyarki ta mutu "? Kisna tayi shiru taki cewa komai ba "ki daina wannan tunanin duk abinda zaki mallaka muddin zaki rasa wani naki ba mahafiyarki ba na banza kema har da kuruciya bancin haka ko fada wani yace kiyi baza kiyi ba ni dai ki faɗa min gaskiya bayan bayanin malamin bai baku wani abu kunci ba "? "babu idan mun taba yi kinsan zan faɗa miki ",to kun taba shan jinin juna ? Kisna tayi shiru tana tunani dan tasan sun taɓa sha "kun taba sha ko ? Kisna ta gyada mata alamun" eh "subuhanallahi shiyasa kuka kasa rabuwa da juna wallahi " dan Allah aunty afra ki taimaka min na auri musa sannan ki taimaka kije min gidansu ki duba min shi wannan azalumin yayi masa dukan mutuwa ko ina ruwansa da rayuwata ?
"Abinda Aliyu yayi masa daidai ne baki ga har kalazir musa ya watsawa mumy ba ke yanzu zaki iya auran mutumin da ya iya watsawa mahaifiyarki kalanzir har yana cewa a bashi a shana suka jiyo Muryar mufeeda a bayansu ."Wallahi ban taba jin na tsani wani halitta a rayuwata ba kamar yadda na tsani ke da wannan yaron ,ke ko mu da ba mumy ce ta kawo mu duniya ba bazamu iya ganinta cikin damuwa ba bare ke wallahi ki guji fushin mahaifiyarki idan nan gaba duniya ta juya miki baya Allah yasa muna raye mu karar da abinda kika shuka da karanshin shekarunki yar banza yarinya kawai mara imani ta k'arasa maganar tana barin dakin ...
Kisna ta rushe da kuka "kowa ya tsaneni a gidan nan ,me yasa bazu fahimceni ba? "Karki damu ki kwantar