Showing 357001 words to 360000 words out of 495987 words

Chapter 120 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt

idan rayuwa da kisna alkhairi ne a rayuwarka da addininka Allah ya karkato da hankalinta gareka idan ba alkhairi bane Allah ya rabuku cikin sauki ya haɗaka da rabonka mafi alkhairi"ameen mumy Allah ya qara miki lafiya "ameen ta amsa cike da farinciki "bari naje na sameta mu wuce kawai jiki a sanyaye mumy tace "to".

Kai tsaye dakin daya san take ya nufa tana kwance a lokacin bacci ya dade da ɗaukarta ya zauna a gefen gadon yana kallonta da kyakkyawar fuskarta ta rame sosai sai dai kyanta na nan bai je ko'ina ba yaji kamar ya kwanta a gefenta ya rungumeta ajikkinsa amman ya kasa dan babu wannan damar a tsakaninsu yanzu wannan damar ta wuceta har abada a hankali ya fara tashinta "kisna !kisna !! ta motsa batare data bude idanunta ba ta sauke numfashi tare da daura hannunta daya akan cinyarsa ta cigaba da baccinta "ke ki tashi mana yayi magana yana dan marin kumatunta firgigib ta farka cikin mayen bacci tana mutsuka idanunta kafin daga baya ta bude su fesa akansa "yaushe rabon data sanyashi a cikin kwayar idanuta?"ki tashi muje gida "nayi me ai na dauka na dawo nan kenan zaka aiko min da takardata ..."


Mmm Sudais
[7/19, 5:33 PM] +234 803 631 5951: 💗💗💗💗💗💗
CUTAR DA KAI
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

Page 54

~TRUE LIFE STORY~

*PAID BOOK*

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim
 
"Wannan  littafin na kudi ne  ,mai bukata karanta shi  zai  tura 500 ta wannan   account number  din  1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an  tura sai a turawa wannan number alert  +234 803 238 4602   domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi  sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne .  "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi  za'a iya tuntu'bar  Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos  lace da kamfala  ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da  chiganvy, voil lace Swiss lace   duk akan farashi mai  sauki ,ga mai  bukatar  siyan ɗaya ko sari  yayi magana ta wannan number 08059623096.

"Sakina !   Sakina !!!  dady ya  shiga   kiran  sunanta  a  mutukar  fusace,  ta fito   da   sauri   qirjinta  na wani  irin  dokawar   da   bata   jin   irinsa  ba , ta tsaya   can  nesa  dashi  ya  cilla  mata takardar  sakinta   " burinki   ya  cika  yau   muradi   ya  sakeki   bisa  umarnina  kamar   yadda  na roki alfarma   agurinsa  a farko  ya  aureki bayan  wulakacin  da  yan'uwa da abokan  arziki  suka  min  na kin amsar   auren   " . gabanta  ne  ya  yanke   yayi    wani      irin   faduwa gabadaya   ta  rude  sai  zufa  ya  shiga   tsatsafo  mata   , gashi  dai  abinda ta  dauki    lokaci  tana nema  kenan  amman  sai  da  taji  wani  qulli  ya tsaya   mata  akan  kahon  zuciya   ,qirjinta  ya cigaba  da bugawa  da wani  irin     karfi   kamar  ana  buga mata  guduma , jiki a sabule ta durkusa  ta  ɗauki  takarda tana dubawa  jikinta  na  kyarma  ,shi  kuwa  dady   zuba  mata  ido yayi   kawai   yana   jin   wani  zallar  ɓacin  rai  na  ratsa  shi  a hankali  hawaye  ya  fara  cika Idanunshi   bai  kai ga zubar  dashi  ba ya fara magana  cikin  ɓacin  rai "na   gode  sakina  da sakayyar  da  kika  min "kin  manta ni ne  ubanki  ,na  ɗauki  dawainiyarki  tun  daga  haihuwarki   har  zuwa sanda  na aurar  dake ga mutumin da nake ganin zaki yi farinciki ko bayan raina   , alfarma  daya na nema agurinki    ki  zauna da  muradi lafiya ki  kwantar  masa  da hankali  kiyi masa  biyayya  amman kika nuna bamu  isa  ba  bamu daraja  a  rayuwarki  ya  tsakaninta  yana  sauke numfashi  sannan  ya cigaba " yanzu  na  sake  tabbatar  da  cewar bakya  qaunarmu  nida mahaifiyarki   duk  yadda  muke  son d'auraki akan hanyar  tsira  kince karyamu tasha karya  bamu  isa kibi umarninmu  ba 'bata  bakinmu  kawai  muke to mun gode mun  gode  amman kisan wani abu  daga  yau  babu ni babu ke  har abada  na  cireki a cikin  ya'yanna  ki  nemi  wani  uban  bani ba  ,Kuma karki   sake   naga  wadan nan  kafafun   naki   cikin   gidan  ki san inda  zaki  dan bazan sake zama dake ba  yana   gama   fadar  haka  ya juya  fuuuuuuu  sauran kadan ya   tuntsira ..."   

ta  rushe  da   wani  irin gigitaccen  kuka   tamkar  wacce  aka zane ta cigaba da  duba takardar sakinta adadin  data  karanta  bazai misaltu ba , yau dai  ta tabbata sakakka  abinda  tafi  komai  bukata fiyye da komai  sai dai ta rasa me yasa abun ya tsaya  mata  a kahon zuciya kuma ya d'aga  mata  hankali   uwa uba hukuncin  mahaifinta akanta shine abinda   yafi  dagula   mata   lissafi  a halin  yanzu  "na  cireki acikin ya'yana  ki nemi  wani uban kuma kar naga  wadan nan   kafafun  naki a gida lallai  wannan  hukunci  ya  tabbatar mata  data   fada  motar  wahala batasan  mintunan  data  ɗauka  agurin  rike  da takardar saki tana juyawa  tana  tunani maganar mahaifinta  wata  irin zabura tayi a matukar    rude tamkar mahaukaciya  ta  nufi  d'akinta  ta fada  kan  gado  ranta  duk  babu  dadi  ta damke takardar  sakin  gam  a hannunta  tana  kuka tana furta kalmar " na shiga  uku  dady  karka  min haka karka  cireni  acikin ya'yanka  ina sonka  dady wallahi nayi ƙoƙarin na juya  zuciyata  ta amshi  muradi  amman na  kasa  kuka take sosai  har da shesheka  .."

tunda  dady   ya shiga mota ya zauna a bayan  mota direbansa yaja  zuciyarsa  ke  tafasa suna  isa gida bai jira direba ya  fito ya bude masa ba ya fito ya  shiga  cikin gidan mumy dake tare  da  sadiq suna hira  tana ganinsa ta mike tsaye cikin tashin hankali dan bata taɓa ganinsa cikin yanayin daya shigo ba, ya fada dakin ya zube akan gado ya rushe da kuka ta rufa masa  baya     tana  shiga  dakin  ta gansa yana kuka jikinsa na bari  nan  ta shiga  tambayarsa "lafiya  meke  faruwa ?" Salaha  sakina  ta cutar da kanta da rayuwarta ta cutar damu   da duk wasu masoyanmu duk tarbiyar da mukayi dakon yi da tattalinta  ya tashi a banza sakina ta rusa komai ta bata komai yau dai nabawa muradi ya sawwake mata aurensa dake kanta karta kashe dan mutane azo ana kuka damu  "jikin  mumy na rawa tace "yan .. yanzu  ya saketa kenan ? ta fada a kidime " Eh  "iyakar abinda mumy  taji kenan ta tafi ta kifa  cike da  daukewar numfashi ya shiga jijigata cikin. kururuwa "salaha salaha  karki min haka "wayyyohhly Allah kisna kin kashe uwarki na shiga uku  kin kashe min mata , ganin kukan  bazai fishshe ba sai kawai ya kwaso  da gudu ya fito falo  yana neman  layin  ya badamasi cikin tsananin tashin hankali yake fada masa abinda ya faru cikin sauri ya karaso cikin gidan dan daman  shigowarsa  kenan  daga aiki shine ya sukunci  mumy  gabadaya ya fito masu  aiki sadiq  da dady suka biyo bayansa  ya sanyata acikin mota yana kuka dady na kuka   ya shiga gidan baya  ya rungume mumy ya badamasi  soma  juya kan mota suka fice ."

Suna  isa  asibitin  ya badamasi aka sanya  mumy  a  gadon daukar marasa lafiya aka wuce daita dan a lokacin ta farfaɗo sai dai wata irin jijiga take kamar mai iskokai badamasi kamar ya zare ya  kasa duba mahaifiyarsa  ya tsays yana kuka a tunaninsa mutuwa zatayi sai  likitoci abokan aikinsa ne  suka rufa akan mumy suka  shiga aikin ceton rai , cikin kankanin lokaci asibiti ya cika makil da  ya'yan  mumy Samir  ne  yazo daga karshe yana zuwa ya isa gaban aunty ummi dake kuka ya riko hannuwanta "lafiya aunty  meke  faruwa ne ? cikin kuka  take ce masa " babu lafiya Samir al'amura  sun  rikice mumy  dai tana cikin  wani  hali  a dalilin kisna batasan  wanda  ke  kanta ba".  ta karasa maganar  tana rushewa da wani kuka yadda aunty ummi ta sheidawa samir haka ta kira number muradi  Wanda  ta samu da kyar ya ɗauka , ta koro masa halin da ake ciki cike da tashin hankali yace "gani  nan zuwa shap shap  ya wuntsulo daga gado ya shiga bayi yayi  wankan janaba   ya  sauya  kaya  ya shiga dakin  kisna  dake kwance har lokacin rike da takarda a hannunta "ki tashi muje mumy babu lafiya wata irin zabura  tayi tana masa wani irin kallo shima sai lokacin idanunsa ya kai ga hannunta bai ce komai ba ya sauko ta  nufi hanyar waje  tana sake damke takardata  suna  isa  taga   halin da mumy take ciki zubewa a kasa tayi tana kuka cikin wani irin tashin hankali wanda bata taɓa  riskar kanta ba aciki ba, a yanzu halin da take ciki bai dameta ba illa lafiyar mahaifiyarta  dake tsakanin mutuwa da rayuwa shima muradi a rikice yake Idanunshi tap da kwalla ya durkusa a gaban kisna "Kinga abinda kika jawo ko ?" ta d'ago idanunta da suka canza kala  tana masa wani irin  kallo na tausayin  kanta , muryarsa a dakushe yake cewa "hakika  kin  cutar min da uwa adalilin mugun halinki  kalli kiga  yadda zalincinki da rashin tausayi da rashin imaninki ya janyo zamu rasa mumy" .  yasa  hannu yana share hawayen da shine karo na farko data ga  yana  kuka akan idanunta wasu hawayen  na  sake zubo masa " .

"Ban taba jin tsanar wani mahaluki ba irinki sakina ban taba jin kinyi min abinda nake jin bazan yafe miki ba sai yau bazamu iya karasa rayuwa dake ba kamar yadda dady ya fada dan bamu da abinda zamuyi dake".  inji cewar ya badamasi wani  sabon hawaye    ya sake gangaro masa  "kin cucemu  wallahi kin cucemu Allah ya saka mana abinda kika mana ki tashi ki bar asibitin nan  bama son ganinki har duniya ta nade babu mu babu ke ki tashi ki bar nan ya karasa maganar yana janta bai tsaya a ko'ina daita ba sai a haraban asibiti ki bar rayuwarmu ".  kisna  ta tsaya bisa kafafunta     tana  wani  irin ajiyar zuciya  da  addu'ar Allah ya tashi kafadan mahaifiyarta  ta kai hannu ta share hawayenta "tabbas ta barwar kanta tabon da bazai taba gogewa ba idan ta rasa mahaifiyarta  bata san tsayin  rayuwar da zatayi cikin kunci da bala'in  abinda ta haifarwa ahlinta ."

bayan ya badamasi tabi a hankali  a daidai lokacin da wani likita ya fito daga dakin da mumy ke ciki  muradi  ya  biyosa  yana  hawaye  sai faman cewa  yake "likita ya mahaifiyata ?
"wani hali take ciki abinda yake iya  furtawa kenan cikin ruwan murya da jiki , gabadaya likitan ya daidaita natsuwarsa  a lokacin da Samir ya karaso a rude Shima yana cewa "likita ta mutu ne ?ya girgiza musu kai alamun a'a  "gaskiya tana raye muna kan iyakacin kokarinmu akan ta dawo daidai ku dai yi mata addu'a ya karasa maganar yana shiga office dinsa ya badamasi ya jingina bayansa da bango gurin  dan rasa abinda zai ce wannan bayanin ya dan kwantar da hankalin kisna ta shigo cikinsu tamkar mara laka tana zazzare idanu  inda  aunty  ummi  ke cewa "mufeeda Allah  ka  bamu ya'ya masu albarka wadan da zasu ji maganarmu Allah ka rabamu  da haihuwar ya'ya  irin kisna "tana  kuka  tana magana kafin a hankali  ta dinga ja da baya dan matsawa daga inda kisna ke tsaye tana zubar da hawaye  gabadayansu  suka dare suka barta tsaye  muradi ne  kaɗai ya cigaba da tsayuwa  yana kallon  kasa zuciyarsa na wani irin zafi gbdy ya rasa natsuwarsa tana nan tsaye Samir ya karaso ya kai mata mari ",tsayuwar me kike yi anan ko bakiji abinda ya badamasi yace ba Bama bukatarki bama son ganinki ki kama gabanki  cikin kuka tace "nima mahaifiyata ce fa  kuma ina damar da zan tsaya tare daita  ". hannuta ya rike gam cikin nashi  ya shiga tafiya daita tana kuka  bai tsaya akoina ba sai a bakin titi ya tsaya yana dubanta wallahi kika sake shigowa  asibitin nan zan mugun baki mamaki  kisna bata d'ago ta kalleshi ba illa ta fashe da kuka shi kuma ya juya ya koma cikin asibiti a hankali ta  dinga tafiya tana kuka "yanzu  akan muradi suka juya mata  baya ?"  tunda take a rayuwarta ba'a taba mata irin wulakacin da ahlinta suka mata ba ,sun wulakanta ta sun tozartata akan bare  amman ta rantse da Allah zata bar rayuwarsu  kamar yadda suka bukata zatayi nisa da rayuwarsu ta cigaba rayuwarta tafiya mai nesa tayi  har ta iso unguwarsu musa anan ma wani sabon tashin hankali ta iske domin kuwa abdulfatai abokinsa ne yake   mata bayani musa na jail tun wata uku da suka wuce  batare da yasan laifin daya aikata ba "
durkyshewa tayi agurin tana rusa wani sabon kuka "na shiga uku ni sakina meke shirin faruwa da rayuwata ?"  Shikenan bani da wanda zai taimaka min "fatai dake tsaye a gabanta ya zuba mata ido kawai yayinda wata irin zufa ke tsatsafo mata a gbdy ilahirin jikinta a hankali ta juya tana tunani  kanta  ya daure tunanin  inda zata take  babu wacce tazo mata sai afra dan haka soma tunanin nemanta  sai dai tunawa da tayi babu waya a hannunta yasa  ta juya da sauri ta koma gurin fatai da kyar ta saita kanta tace  "dan Allah ara min wayarka zanyi kira dashi " nan da nan ya bata da yake ta haddace  number  afra  sai ta hau kira tana  jin  ta dauka ta sakar mata kuka "aunty  afra na shiga uku  afra na jin kukanta  ta saki murmushin jin dadi dan tasan dole ta nemeta  dan tun awa biyu da suka gabata  suka ji batun mutuwar aurenta  da halin da mumy take ciki har ma da hukunci dady,  dad dinta  ma bai jima da fita zuwa  asibitin ba sai dai cike da makirci afra tace "kisna lafiya  ?"me yake  faruwa ?"cikin kuka take cewa ba lafiya ba aunty afra  komai ya kwabe min muradi ya bani takarda sakina sai dai adalin haka mumy na kan gadon asibiti gashi dady ya sallamani  in fact  ya  cireni acikin ya'yansa ga musa a jail  ta karasa maganar tana rushewa da kuka "yanzu ya za'a yi kenan ? "wallahi ban sani ba  ,ban san inda zani ba "Ya kamata  kiyi tunanin inda zaki Kinga. tunda dady ne yace ya  koreki duk wanda ya amsheki a cikin dangi zai iya haifar da gagarumin matsala ki samu inda kika laba ko acikin family musa ne  kafin abubuwa suyi sauki". "Bari nazo gidan Hajiya mu hadu mu zauna tare tunda bata koreki ba ai bazata koreni ba "kiyiwa Allah kiyi hakurin kin san daman can ni mai laifi ce idan kuma zaki zo na tattara nasan inda dare yayi min "jiki a sanyaye kisna ta zame wayar a kunneta  ta mikawa fatai ta soma tafiya ."

  bayan  kisna ta kashe wayar  aunty afra tayi wani irin juyi acikin dakin da  granny ta bata  tana cewa "kadan mumy  ta gani ba dai ta iya danne laifin ƴaƴanta ba ta hangi nasu  tare muka  aikata laifi  da kisna amman dan zalinci sai  tayi murna da sakin da badamasi  yayi  min yau kema ga naki sakamakon nan an saki kisna kuma muddin ina raye kisna ta bar rayuwar Aliyu kenan yadda banyi rayuwa dashi ba itama bazata koma garesa ba   da sannu zan cigaba da dauraki akan hanyar  da bazata bulle miki  ba bazaki  fargaba har  sai lokaci ya kure miki ".muradi kuwa tunda Samir ya fitar da kisna hankalinsa ke tashe yayi tunani iri iri akan inda zata bai hango ba  kawai yayi tunanin ya kira habib da hanzari ya kira shi a waya yace" maza ya taimaka ya taho ta gurin asibitin ya badamasi ko zai hadu da kisna  ka ɗauketa kaje ka kama mata hotel ko nawane zan biya "friend lafiya  kuwa meke faruwa ?"  muradi ya runtse idanuwansa ya bude muryarsa dake a dakushe ya shiga yiwa Habib bayanin duk abinda ke faruwa har da kwalla, nan Habib ya haɗe rai tamkar yana gaban muradi yace"yanzu akan wannan mara mutunci yarinyar ka shiga damuwa har kake kokarin taimakonta ? Muradi yace darajan iyayenta ne " .
"to gaskiya ni bazan wani iya taimakawa  ba  Allah ya bawa mumy lafiya sai nazo  ya katse wayarsa , muradi ya sauke naunauyen ajiyar zuciya yana   furta "ya Allah ya kira jahid shi kam  babu yadda  zai yi yace "to Shikenan Allah yasa na ganta "na gode jahid "babu komai muradi yiwa kaine nan da nan jahid ya shiga motarsa ya biyo hanya sai dai babu inda bai duba ba  bai ga kisna ba ya kira muradi nan fa hankalinsa ya qara tashi ya shiga tunanin ina ta nufa ya dai nasan musa baya nan to ina zata ?"Zariya ya shiga yi zuciyarsa na wani irin zafi shi kansa zazzafan zazzaɓi yake ji amman ina bazai iya kwanciya ba har sai yaga makomar mumy cikin ikon Allah awa uku da shigar da mumy aka turota a gadon marasa lafiya  tana baccin  da aka
nemammta dan hutu gbdy suka rufa mata a baya cikin farinciki saboda  ganin tana numfashi  aka shigar da mumy daki na musamman aka daura mata ruwa  a jijiyar hannunta gbdy suka zagayeta  suna mata addu'ar samun sauki ".

Kusa  awa  hudu kisna na tafiyar   kafa batasan inda zata dosa ba a  cikin gidajen yan'uwa kawai ta yanke shawarar komawa gidan muradi shi zai fi mata sauki kafin ta samu gurin ra'bawa  ta kwankwasa kofar karamin get mai gadi ya leko ta karamin huji ganin itace yayi saurin bude mata ta shiga jikinta a sabule kai tsaye dakinta ta nufa ta  kwanta ta rasa yadda  zatayi  ,ta  rasa abinda ke mata  dadi komai na duniya ya tsaya mata  me ya kamata tayi   ?" Zuciyata  ki fada min abinda ya kamata nayi ....?" Har dare ya fara yi tana kwance tana tunani mafuta tana son dole kafin wayewar  gari ta samowa kanta mafutar  abun yi domin cigaba da sabuwar rayuwarta sai dai har asuba bata runtsa ba haka zalika bata samawar kanta mafuta ba .."Karfe bakwai daidai na safiyar ranar muradi  ya shigo gidan  direct d'akinsa ya shiga sai dai ya tsaya yana kallon dakin tun daga inda sa'insarsu ta jiya ta fara har zuwa sanda ya makata akan gadonsa  ya kai idanunsa kan gadon nan take komai ya shiga

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login