Showing 114001 words to 117000 words out of 495987 words

Chapter 39 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt

sake furta min wata kalma sai na harbeki yanzu ya ciro bindigasa daga aljihunsa yana nuna sautin brain dinta da kyar mumy ta hadiye kukanta  dan ganin halin da yayanta suke ciki yau ta shiga tsakaninsu tana bawa ema hakuri saboda tasan halin  zuciyarsa zai iya aikata komai  hayaniyarsu tasa  Sadiq ya  barke  da kuka yana wuntsil wuntsil da kafafunsa ta dauki danta ta rungume  tana rarrashi shi kuma sai tsula kuka yake "yar iska ki tsaya kina bata  rayuwarki akan mutumin da bai san komai ba sai ashararanci mara cikakken ilimi ko ke mai kashe kanki ce ki huta akanshi bata sake tanka masa ba har ya bar dakin yana surutai mumy ta kamota ta zaunar daita tana kuka "dicter ki taimakeni ki kai dan nan gurin  ubansa ko dangin ubansa mu zaman lafiya bazan iya daukar wannan maseefar ba ,a hankali mumy ta dinga mata magana wanda Sam baya shigarta dan bataji zata bawa haroon karamin danta koda zai amsa bare ya nuna bai so ....."

   A  daidai  wannan lokacin da al'amura  suka dagule  mata   ta kowani bangare   babu sauki daga  yan'uwa  ta ko'ina zafi  ne  ,  ta samu labarin inda  haroon  ya koma a bakin  wani  abokinsa commander    bata  yi sanya  a gwiwa ba ta amshi  full address din inda  yake  ta tattara kayanta batare da tayiwa kowa sallama ba   ta  nufi  Abuja ta sauka  a  yanya   bata sha    wahala gano  inda yake  ba tashin farko  yayi  mata hauka amman  daga karshe dole  ya  hakura ba dan ransa  yaso ba sai dan abokansa   da suka saka baki   tare  da kai maganar  gurin Chirman,   chairman na  gama jin dogon  bayaninta tausayinta  ya kamashi har kwalla ya zubar yace  "yanzu me kike son ayi ?muryarta  a raunane tace  "idan da hali zan so ya aureni  dan a shirye nake dana  amshi  muslimci  chirman  ya numfasa kana  ya  kalli haroon "kai yanzu wannan  ba abun alfahari  bane  agurinka ta sanadiyyarka  wani ya musulunta  "? Haroon Yayi  shiru yana tsotsa keya  sai dai zuciyar nan nashi  tamkar  ta kama da  wuta"kayi tawakalli ka yarda da hukuncin Allah  kasan baka shirya haihuwa ba mai yasa ka kai kanka ga aikata zina ? Muryarsa a dake yace "bani  na mata cikin ba  taje gurin wanda ya mata  dan  tasan uban danta  amman bani haroon ba ..

  "kayi wa zuciyarka   adalci haroon  duk  wanda yaga yaron nan  yasan danka ne ka hakura  ka rungumi rayuwarta   ko dan darajan jininka , chirman ya  dauki  dogon lokaci yana  masa nasiha a karshe  ya muslintar daita  ya  tara mutane aka   d'aura  musu aure , abokansa    isa   sule tare da  Usman  suka kaita madaidaicin   bukkansa  da  yake  rayuwa aciki a bayan  gari  ,babban filli da  wani  ma'aikacin gwanati  ya bawa chairman  ajiya shine kowanensu  ya  dibiba  yasa  aka  rufe da tambal aka  maidashi  daki  sai dai  shi  yasa an cire masa  bayi daga gefen d'akin sa  ."

Da  misalin  karfe shida  yamma  ya shigo dakin lokacin  daya  daura idanunshi  akan yaron dake  kwance a saman  cinyarta   gabansa  yayi mummunar  faduwa saboda  tsantsar kamaninsa  da yaron  dan  duk haukan da yayi bai tsaya yayiwa yaron kallon  tsab ba ,guri ya samu  a gefen katifa ya zauna  tare da rafka tagumi  ya zuba mata ido  yana  kallon kyakkywar fuskarta  tana jijiga yaron  lura  da tayi da irin kallon da  yakewa yaron yasa ta yunkura  ta d'aura yaron akan  cinyarsa ta fice daga d'akin  ta shiga bayin  dake manne da bukkan  tsaf an sumenteshi  da breaking tayis  hannu  ta  kai ta jijiga  jarkan da ta gani a ajiye  a  bayin taji motsin ruwa  ta tsiyayya acikin wani  karamin botiki da ta  gani sannan ta durkusa  domin yin fetsari ,koda  ta dawo dakin  idanunsa na kan sadiq  ya  riko yatsun hannunsa  yana kallonsa komai  nashi  ya dauko  babu  abinda ya dauko na  mahaifiyarsa sai duhun  fata   , wani irin abu  yaji  yana bin jijiyoyin jikinsa , zama tayi  ta fuskanceshi ya ɗan  d'ago kanshi ya kalleta  sannan yace "me zaki ci ?wani  irin yanayi ta  tsinci kanta , zuciyarta  tayi sanyi cike da  jin dadin maganarsa duk  da tasan bai taɓa sonta ba itace ke haukan sonshi  amman taji dadin furucinsa na yanzu ,murmushin jin dadi tayi tare  da sake  kallon inda yake  zaune a takure  rike da  sadiq gabansa na  faduwa ,matsowa tayi kusa  dashi ta riko hannunsa  daya, a hankali  tace " haroon  i love You ,i really love you haroon  tun daga lokacin dana  fara faɗa maka wannan  kalmar da gaske  nake yanzu ina sake maimaita maka ina sonka  ba dan kudi ko ilimi da dukiya  ba, ka soni karka dauki  alhakin  zuciyar da ke  maka  soyayyar gaskiya da gaskiya numfashi  ya fesar  cikin  tsananin  zafin nama ya zare  hannunsa ya daura sadiq  akan  cinyarta dan idan  akwai abinda yafi tsana  yaji daga bakinta bai wuce wannan shirmen  banza ba zuciyarsa  a dagule yace "baki  da wata amsar data wuce bana sonki kuma  bazan taba sonki ba  har abada sannan nan  kusa zaki nemeni ki rasa  bazaki  sake ganin koda inuwata bace a rayuwarki , gaban dicter  wacce  ta  dawo rashida a wanin da suka gabata ya   dinga  faduwa bakinta ya kasa furta komai   tana kallonsa ya fice  daga dakin sai jin motsin  ruwa tayi hakan yasa  ta fahimci wanka yake  cikin mintunan da basu  wuce  goma ba , ya dawo  dakin daga shi sai dogon  wondo  baki ya dauki towel ya goge jikinsa  tana zaune tana kallonsa  har ya gama shirinsa  ya  dauki  riga army  green  da wondo baki  ya saka ,ya d'auki wayarsa  yasa a aljihu  ya fesa  turare infenity  sannan  ya  kalleta  cike da  tsananin kiyayya yace "ki fadi abinda zakici akawo miki idan dare yayi ki kulle ko'ina saboda  bazan dawo ba sai  gobe zuciyarta na bugawa kamar zai fito waje saboda firgici  ta yunkura ta saba danta a kafada wani irin tashin hankali ta sake shiga gabad'aya jikinta yayi sanyi  bai tsaya jin abinda  zatace ba ya sa kai  ya fita tabi bayansa da  kallon "da gaske dai haroon baya sonta   ta dinga  jin zuciyarta kamar  zata tarwatse saboda  tsabar zafi "dan Allah  ka soni zafin yayi min  yawa da me zanji  tuni  hawaye  suka wanke  mata  fuska ,a gurin  yan'uwansa babu sauki agurinka ma  haka  kusan wannan tashin hankalin yafi komai  ciwo da rad'ad'i  a zuciyarta ta kamkame danta ajikinta tana  wani irin kuka shima kuka ya fashe dashi  kamar  yasan uwarsa  na  cikin damuwa , kuka  tayi sosai bayan  kamar minti talatin  taji motsi ana sallama  ta kwantar da danta  ta fito daga cikin bukkar  wani  matashin yaro  ta  gani tsaye ya gaisheta  cike da girmamawa  sannan ya mika  bakar ledar  "gashi inji  oga tasa hannu ta amsa  tana masa godiya ya  juya ta dawo cikin bukkar  ta buɗe laidar takeway  ta gani da ruwan  Eva da pure water guda  biyar  masu sanyi ta  sauke  ajiyar zuciya sannan  ta zauna ta soma  cin abinci bayan ta  gama tayi wanka shi kuwa  sadiq sai  goge masa  jiki tayi saboda babu  ruwan zafi  gashi babu  risho a bukkar bama  risho  ba duk wani abun  amfani babu a gurin  ,bukkar daga katifa sai  fanka da kwan lantarki sai school bag d'insa  da jakar kayansa dake  gefe ta ciro wayarta  ta jona cajin wayarta  ta kulle  kofar saboda  dare ya soma dan bakwai ta wuce da wasu  yan mintuna   ..."
  Kamar  yadda   ya fada mata  bai dawo ba sai washegari  ya dawo motsin  bugun ko'farsa ya tadata ta mike ta bude masa kofar tayi masa sannu da zuwa sannan ta  matsa domin bashi hanya ya raba ta gefenta yana cire facing cap d'insa  ya ajiye  ya fada saman  kafita ya soma bacci  bai  tashi ba sai kusan  azahar yayi Sallah ya   kira  yaronsa  isele ya kawo   mata   abinci shi kuma   ya  cigaba  da baccinsa  bashi ya tashi  ba sai karfe shida na yamma  yayi wanka kamar  jiya ya fita a qalla sai  datayi kwana bakwai wata  mu'amular arziki bata shiga tsakaninsu ko motsa  bakinsa baya yi haka  baya kallon inda take  bare sadiq da yake ganin  shine babbar matsalarsa  a arayuwa, duk abinda yake yana damunta  amman  bata da  yadda zatayi  dole take yin shiru ranar data cike  sati biyu a bukkar  ranar ta  kudurta aranta zata shiga kasuwa ta siyo  abubuwan bukata lokacin  da  yaronsa asele      yazo   kawo  mata  abincin   tace  zata bishi  ya nuna mata kasuwa  tare suka fita ya kawota  kasuwa  tayi amfani  da atm  d'inta ta  siyo  kayan amfani tukunya  da slinder gas  da  duk abinda tasan zata  bukata haka ma ta bangaren Sadiq ta siyo masa Pampers da madara dan nono baya isansa , koda haroon  ya dawo gida domin  shirin fita muguwar kasuwancinsa  da yasa kanshi   ya  firgita matuka  ya dinga  mata wani irin kallo kafin daga baya yace  "ke mene ne haka nake gani ance  miki zama kika zo ne  ko me  "?
"Lokaci  na baki  fa yana cika  zaki  koma gurin iyayenki  kisan yadda zaki    daidaita dasu su amsheki da danki   dan zamanki cikin  rayuwar haroon daidai  yake da siyawa kanki  ticket din mutuwa cikin  tsoro tace "dan Allah  kayi hakuri ka  barni gara na mutu tare da  kai wallahi ina tsoron abinda  yan'uwana zasu yi  min sannan banason sadiq  ya taso yaga irin tsanar  daake masa adalilin  zunubin iyayensa  ta karasa maganarta   tana  kuka lumshe  kyawawan idanunshi  yayi  sannan ya  buɗe ya daurasu akan sadiq  dake kwance yana wuntsil  wuntsil da kafafunsa "me kika ce sunan  yaron "?
"Sadiq  ta  furta tana kuka  ya girgiza  kai  aranshi  ya  furta" wallahi  dicter kin haukace  a zahiri kuma yace " ubanwa yace kisa wannan dan naki suna to bari kiji ko sunan ubansa zaki saka masa bazan amsheshi haka zalika dangina bazasu amsheshi ba dan haka tun wuri ki kama gabanki dan bazaki yi rayuwa mai dadi    dani ba saboda da  gaske bana sonki "cikin tsoro tace "dan Allah ka daina cewa baka sona  kalli  irin kyautar da Allah  yayi maka adalilina,  kayi  hakuri kayi  alfahari dashi koda bazaka  soni  ba ka daure ka .."Babu abinda zaki samu agurina fa hankalina bazai taba  kwanciya dake  da   wannan dan naki ba wannan dan naki na bar miki shi har abada dan  bani da abinda zanyi dashi   ya soma cire kayan  jikinsa  yana jifa dashi sannan ya fita tana  tsaye kamar an dasata  ."

ta  dade tsaye tana tunani  har sanda yayi wanka  ya shirya cikin jallabiya  brown  ya daura facing  cap  baki da takalmi  baki ya fice  washegari  ma haka ya  shigo da safe  tana zaune  tana karanta littafi addu'oi  mai fassara da  turanci ,duk da bata sallah  har lokacin amman  tana fahimtar wasu  abubuwa dangane da  addani , shi wanda zai  tsaya ya koya mata bai  natsu ba bare tasan yadda  zata tsaida addininta  gabansa na tsananin faduwa ya fada saman  katifa ya kwanta a gefen  sadiq yana kallon  fuskarshi photo capy  dinsa sak jikinta a sanyaye  ta rufe littafin hannunta  ta hau saman katifar  cikin tsoro tace" sannu  da zuwa banza yayi  mata ya runtse idanunshi  ta kai hannunta  jikinsa "bari nayi  maka massaging da  alamun ka gaji dayawa   nan ma shiru yayi  ta kai hannunta jikinsa  ta soma mammatsa  masa jiki zuwa  nipples  d'insa  wani  irin sanyi yaji yana bin  sansar  jikinsa saboda  dadin abun daman  kuma yasanta da yadda tasirin hannunta suke  gurin  iya  massaging  kafin kace me  tuni yanayinsa ya soma  sauyawa  jin idan bai yi wani abu ba komai zai iya faruwa yasa ya mike  daga kan katifar ya zira  slippers akafarsa ya shiga  wanka ya fito ya sake  kwantawa bata daddara  ba ta sake kusanto  jikinsa tun yana dojewa  sai gashi yayi balance  cikin kankanin lokaci  ya  birkice mata zuwa wani  yanayi na dabam  bai  san abinda ya  aikata ba sai bayan daya  gama  sannan ya hankalta  aiko  ya rufeta da  ruwan bala'in zatai magana  yasa hannu ya d'agota  ya  ɗauketa da wani  gigitaccen mari har guda  biyu sannan yaja tsaki   tayi  dariya "banyi danasani  ba  sannan ban  ji haushin marin ba da  sannu Allah zai min maganinka  dan banga dalilin  da yasa zaka dinga min irin wannan kiyayyar  ba ,ka gaugauta tuba  akan abubuwa da kake  min sannan ka canza  rayuwa  domin wannan  rayuwar daka daukarwa  kanka wata rana  zakayi danasaninta , ko kuma nace  zaka cutar da kanka  sannan mutane irinku  sune suke hana duniya  kwanciyar hankali  ina tabbatar maka  daga rana mai kamar  ta yau ka dinga kuskuren  kusantata kenan  ina addu'a  a dukkanin   shafukan rayuwata  ya zamanto nice  uwar ya'yanka a nan  duniya  duk  macen da zaka  kusanceta spam dinka  ya zamo ruwa mara  amfani  ajikinta "ai kuwa kisawa ranki kinyi bankwana  da farincikin sannan  zan ladabatar da kazamar  zuciyarki banza shasha  kawai mara mutunci  da kamun kai ana  gudunki kina naci "komai  zakayi  kayi a shirye  nake  kuma  bazanji  haushi ba  kai yanzu  nafi bukatar kiyayyar   akan  soyayyar dan tafi  dadi  ,banza   yayi  mata yayi  kwanciyarsa  bai tashi ba sai  lokacin da fitarsa tayi ."

******
Akwana  a tashi babu wuya   agurin  Allah  sai gashi  har dicter  tayi wata  biyar  wanda yayi daidai da watan sadiq tara  a  duniya  yana gudunsa  ko'ina haka yana  gane babansa daya ganshi  zai yi ta daga masa  hannu  ,wata  rana ya daukeshi wata rana yaki   kuma a wannan lokacin ta fuskanci ciki gareta  ta shiga damuwa sosai   sai  dai  tayi farinciki  sosai aikuwa lokacin data  gaya haroon taci wani  abu wai shi duka ,duka  yayi mata kamar  zai kasheta tare da  yi mata saki biyu   yana  furzar da  iska mai zafi daga bakinsa  "daman ni  ban ɗauki aurenki da wani daraja ba dan dashi da babu agurina  duk daya ne ,itama kusan hakan ce gareta sai dai ita ta yarda ta zauna karkashinsa  ko ta wani hali ya dawo gallaza mata hatta dan  abincin da yake bata ya daina wulakanci yau dabam na gobe dabam har bukkan yake kawo yamnatansa ya korota waje yayi iskancisa dasu duk ta kawo ido ta saka masa , kudadenta  dake cikin account d'inta kuwa sunyi kasa sosai sai manage take damuwa ta taru tayi mata yawa saboda rashin samu cikakken kulawa ga yaronta karami ga cikin wata uku , haka tayita rayuwa acikin bukka  a hankali har suka saba da isele gefe guda kuma  cikinta na girma ,wata tara cif ta haihu ita kadai kamar haihuwar sadiq ta samu danta namiji shima mai kama da ubansa sak har ma yafi kama dashi akan sadiq saboda shine ya dauko farinsa sosai da tsarin jikinsa wannan haihuwar babu abinda ya kara mata a zuciyar haroon kamar bakin jini da zalar kiyayya suna zaune a daki isele ya shigo bakinsa ɗauke da sallama ya dauki sadiq ya daga shi sama yana masa wasa shi kuma yana bulbulamasa dariya  "kayi kani sadiq ka rage kiriniya  ya fada yana kallon haroon oga wani suna aka sawa baby ne"?"Ban sani ba kuma karka dameni "esele ".
Dicter ta kira sunan  esele " me ye sunanka na gaskiya  ?Yayi murmushi sannan yace "Aliyu ""Ka iya radawa baby suna a muslinci ? yace mata "eh "Okay rada masa  suna da Aliyu take esele yayiwa yaro   huduba da Aliyu shi kuwa haroon ko ajikinsa shirinsa yake hankali kwance ciki farar riga mai gajeren hannu da bakin wando yana gamawa  ya daura facing cap d'insa na gado ya fice.esele ya zauna cike da jin dadi , a hankali dicter ta dinga jansa da hira daman kuma sun saba sosai dashi tace "esele Wai aikin me haroon yake yi ne da bai kwana a gida  kullum yana garaji "?
Shiru yayi mata  har sai data sake magana sannan ya tsosa gaban goshinsa "a zahiri gaskiya aikin da oga yake ......nan ma ya sake yin shiru "ka faɗa min mana  karka boye min komai  ka ɗaukeni kamar yayarka nima kuma kamar kanina na daukeka aikin me haroon yake ?"A zahiri gaskiya oga dila coken ne wato   hudar  iblis ............."

MMN SUDAIS[7/19, 5:32 PM] +234 803 631 5951: 💗💗💗💗💗💗
CUTAR DA KAI
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

Page 19

~TRUE LIFE STORY~

*PAID BOOK*

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim

"Wannan  littafin na kudi ne  ,mai bukata karanta shi  zai  tura 500 ta wannan   account number  din  1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an  tura sai a turawa wannan number alert  +234 803 238 4602   domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi  sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne .  "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi  za'a iya tuntu'bar  Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos  lace da kamfala  ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da  chiganvy, volyal lace  duk akan farashi mai sauki ,ga mai  bukatar  siyan ɗaya ko sari  yayi magana ta wannan number 08059623096,


......." Koken ta furta a mutukar firgice tare da dafe qirjinta da duka hannuwanta , a tsoroce esele yace" ki rufa min asiri maman sadiq kada ki bari oga ya san na faɗa miki business dinsa zai iya ... .." saurin d'aga masa hannu tayi jikinta na kyarma "Karka damu esele babu abinda zanyi na gode sosai daka faɗa min gaskiya amman kaima shine sana'arka kenan "?Yayi saurin gyada mata kai alamun "eh " shiru tayi tana kallonsa zuciyarta na tsinkewa bata san sanda hawayen bakinciki suka zubo mata ba "ki daina kuka maman Sadiq da nasan zaki shiga damuwa a dalilin maganata wallahi ban

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login