Showing 174001 words to 177000 words out of 495987 words

Chapter 59 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt

ido suna Kallonta cike da mamaki . "zaki  zo  da wahalar kenan ko  ?  inji cewar madu  "ai kai ne wahalallen  tayi saurin dakatar dashi   ,kun  wani zo nan  kuna ta ɗaukar  hoto ko a samu wanda zai  kirani   ai nasan duk sharrin  wannan ne  ta  k'arasa  maganar tana nuna  Samir "sannu  gimbiya saboda ana  jin tsoronki ne  za'a zo  kiranki  alhalin kinsa hakan zata  iya faruwa  dole idan anzo za'a yi hoto , ke da   kika san kina son d'aukar  hoton me  yasa kika ....."?

"Ya  isa  abar  maganar haka  inji cewar  ya badamasi  zo nayi miki hoto my   queen ya  ciro wayarsa iPhone xx max   , tabe  baki Samir yayi tare da cewa " yar  wahala  kawai   ke dai  idan baki ja mutane  faɗa  ba  bakya  jin dadi yar rainin hankalin kawai ". hotuna  sukayi sosai daga karshe  tasa ya badamasi  ya siya  mata  wani  ice  cream   ,Samir   ya dauki  ice cream   mai  chocolate  da  kayan motsa baki "bari  na d'aukarwa  muradi  ".da  sauri  ta  matso kusa dashi  ta  tsaya  "ka jika da  iyayi  yana son  sha me ya  hana shi zuwa "?"Ina ruwanki  da rashi  zuwansa ko  kice   zakiyi  kayansa  zuwa gida"?Tace "kai  ne zaka yi kayansa amman dole nayi magana tunda bakina ne  ta fada tana  yatsina fuska "to babu ruwanki dani  idan ba haka ba  zamu raba hali yanzu anan  "to mu raba mana sai me tsoronka  nake ji "?"Kufa gayawa yarinyar nan  ni ba sa'anta bane idan ta raina  kowa karta ce zata rainani   ..."
ya   badamasi  ya  riko mayafinta
"muje  my  queen Samir  fa kaninki ne ki  daina  biye masa fixge mayafinta tayi  tana masa wani kallo "ta ina ya zama  kanina bayan akwai wattanni a tsakaninmu  ya bani wata biyar  fa ta karasa   maganar  tana nuna masa yatsunta  biyar "naji  ni ba wannan nake  nufi  ba  idan lokaci yayi zaki fahimci  abinda nake nufi ya sake janta   Suka  nufi  inda motarsu take  Suna shiga  haraban  gidan ranta yayi bala'in   ɓaci saboda cin karo da fuskar muradi  da tayi cikin shirin  zuwa  masallacin  sanye cikin  jallabiya  baka  kafin  ya karaso inda  motar  take  pake  ta  jefa masa wani  mugun   kallo  tana harararsa tare da  jan  tsaki ta   runtse  idanuwanta   saboda  bata kaunar   ganinsa  a rayuwarta  ya ɗan tsaya yana jiran fitowar Samir   ta  fito  daga  gaban  mota tana yatsina fuska    haka nan  taji zuciyarta  ta  bugu  lokacin da tayi  kusa  dashi  ".
Aunty  ummi ta  fito  da kyar   muradi ya  mika mata hannu alamun ta miko masa  Kisna  "yauwa muradi  dan  Allah  kai  ta dakin mumy  suka jera tare da Samir yana fada masa yazo masa da ice cream kai tsaye dakin mumy  suka  shiga ya  kwantar daita akan  gado ya cire mata takalmi dake sanye a kafafunta  Samir na bashi labarin inda suka je suna ƙoƙarin  fita daga dakin mumy ta fito daga bayi tace "yauwa muradi zo nan kai kuma Samir kira min ummi har da madu ma ya fito cikin sauri tare suka dawo Mumy  ta  kalli muradi tace "abinda nake son fad'a maka  duk inda kaga kawunka garba ko bature    Karka kallesu bare su  ganeka ,  kuma bance ku fadawa wani  daga cikin dangina dake  garin nan cewar an ga muradi ba "  gaba-dayansu suka gyada mata kai alamun sunji "oya kuje kuyi sallah suka fita ummi ta nufi dakinsu su kuma suka wuce massalaci ."

karfe   bakwai  daidai duk suka hallarar  a parlour  Samir ya mikawa muradi  roban ice cream din daya zo masa dashi  ya amsa ya  bude  yaga ice cream din ya narke duk yayi  kunfa  daga sama  ,Samir dake zaune gefensa ya leka cikin roban  saurin dafe  goshinsa yayi "ya narke ko ?  amman banji dadi ba wallahi  shi yasa nace kasha kafin kaje massalaci kaki". ita kuwa afra  ranta fesa da jin abinda Samir yace  "Allah  ya  qara ai ka iya gulma  da iyayi gara  daya narke naga  karya sha   ta  mike  daga  zaunen dake ta shiga Zariya  a cikin parlour'n tana jin dadi   saboda  hango  ɓacin rai  mai tsanani a kwayar idanun muradi,a hankali muradi ya  ajiye roban ya   tashi ya bar gurin ya koma dakinsu  yana  danne zuciyarsa dake masa zafi yana da tsananin  hakuri amman zuciyarsa  bata  daukar wulakaci, yana   da juriya amman kuma yana da   taurin  kai  mai tsanani  akan  abu , idan ya kafe akan abu ko me  zai faru sai dai ya faru  amman  bazai rusuna ba shifa  akan afra za'a iya  nemansa a rasa   gara  yayi  rayuwarsa   a wani bagiren  da  bai da kowa kuma babu wanda yasanshi zai fiyye masa kwanciyar  hankali hawaye ya zubo masa  saboda  baya qaunar rayuwar waje  kullum zuciyarsa na cike da tarin bakinciki rashin sadiq a kusa dashi  baya  son wannan yawon da  yake   " Samir ne ya shigo dakin yaga ya haɗa kanshi  da bangon dakin yana sheshekan  kukan  zuci  dana  zahiri  dan  yana hango yadda bayansa ke motsawa  , ya  zuba wa  bayansa ido kafin daga baya ya karaso gurinsa ya dafa shi  tare da  juyo  dashi suka fuskanci juna   muradi ya tsura masa ido yana huci qirjinsa har dagawa yake , tsawon  mintina ko motsi bai yi ba  bare a saka rai zai yi  magana   illa dauke  hawayensa  da yayi  ,a  fusace Samir yace "wai  bazaka takawa yar iskar yarinyar nan  burki ba ta fita harkarka  dan fa taga kana kyaleta ne   kazo  muje kaci ubanta ya janyo hannun muradi  yana ƙoƙarin fita daga   dakin   amman fur muradi yaki takawa ya tsaya  Samir ya juyo ya zuba masa ido cikin ɓacin rai "ka kwantar da hankalinka Samir  ni gidan ma zan bar mata   rayuwata  bata son yawon   damuwa  "idan ta isa tasa ka bar gidan nan  shege nake  ai ba da kudin  ubanta a gina gidan  nan ba bare ka barshi saboda ita," itace zata tattara ta bar gidan  ta koma gidansu  ka daina raga mata yar iskar yarinya ce wallahi , baka ga tunda naci ubanta muka dawo daidai daita ba , muradi ya sake tsurawa Samir ido a zuciyarsa  yace  "bazan iya cacar baki   da  mace  ba bare dambe  tsakanina da mace ido ne , Samir  ya dade yana rarrashin muradi ganin yadda ya shiga damuwa yasa muradi yace  "zan  zauna darajan wannan soyayyar da ka nuna min kadai ta hanani aiwatar da abinda zuciyata ke gaya min akan zamana a gidan  nan rungumeshi Samir yayi yana sake jin kaunar muradi a ransa   ."Kowa a gidan yana ji da auta Kisna da sun dan samu dan canjinsu akanta yakarewa , shima muradi yana son daukarta dan Allah yayisa da son kananan yara sai dai Kisna bata yarda dashi tana ganinsa zata gudu shi kuma ya bita yana ɗaukarta zata fashe masa da kuka dole zai sauketa yana qaunar daukarta amman bata yarda dashi".


  Afra  na    gama hutunta  ta tattara  ta koma  gidansu    ba dan ranta yaso ba, dan  taso ta  zauna  ta cigaba da  takurawa  rayuwar  Aliyu  wanda bai san ma tana yi ba  ,  komawarta gida ya  haifar mata da zazzaɓi dan ranar data koma a daki ta wuni zur kwance babu inda ta fito har zuwa washegari haka ta dinga Allah Allah su sake samun wani hutun tattara ta koma gidan Alhaji realwan  dan taji dadin zaman gidan  ,zuwa  ya badamasi biyu gurinta kuma a  lokacin ya shaidawa dan'uwan mahaifinsa cewar yana son Afra  da aure idan ya gama karatu yayi hakan ne dan kar abawa wani kafin ya dawo tunda yawanci a gida ake zabawa yaran family dinsu miji , alhj marwan yaji dadi sosai ya tabbatar masa Afra  bata da wani miji  sai shi inshallahu  ,zuciyarsa  cike da farinciki  da soyayyar Afra  ya koma kasar Australia ."

Aliyu ya samu sauyi rayuwa  sosai  domin  kuwa  da za'a koma makaranta  dashi aka koma don  cigaba da   karantunsa na gaba da primary  sai dai an sha fama dashi ranar dan  lokacin da aka tambaye dady   sunansa dana mahaifinsa dady yace " haruna Aliyu take muradi   yace a'a  " benedicter rashida  Aliyu  yake amfani dashi  Alhaji  realwan ya girgiza kai yana murmushi sannan ya ciro wayarsa  ya  kira mumy tace " ka barshi a yadda yake so din ko  kuma yayi amfani da sunan dasu Samir suke amfani  dashi " kina nufin sunana ?tace "eh  " hakan  fa bai yi ba  duk lalacewar haroon mahaifinsa ne taya zaki ce haka ? "ya zamuyi  kenan nasan halin muradi  da kafiya can ilo ma haka aka sha fama dashi kar  a zo ana samun matsala ne Alhaji realwan yace "zakayi amfani da sunana ?muradi ya gyada kai alamun "eh "tun  a ranar muradi   ya canza  Komai nashi zuwa  sunan Alhaji realwan, ajinsu    samir aka saka shi   saboda  tabbatar da kokarinsa da malamai  sukayi ."

sannu    a hankali  aka sake  samun  wani  hutun  zango shekara wanda zasu yi wata biyu kafin su koma  makaranta , a wannan zuwa hutun da afra  zatayi ne ta  tabbatar wa mahaifiyar idan taje  gidan Alhaji realwan  taje  kenan bazata sake dawo ba sai dai  tazo  kawo mata ziyara   nan take  mahaifiyarta  taki  yarda da  wannan tsarin  tace "sai  dai  taje hutu ta dawo amman batun zama gabad'aya babu shi  , ita  kuma tace  "bata yarda da zuwa  hutu kawai ba tafi son zama  gabad'aya   ai kuwa mahaifiyarta  tace sai dai ta hakura  gabad'aya, suna  cikin  wannan hali   Alhaji  realwan  ya kawowa   d'an'uwansa   ziyara  da yammacin ranar ,  domin tautaunawa  akan kasuwancinsu na kasashen  duniya dana nan gida  Nigeria,  yayi murmushin jin dadi a lokacin  daya ji rigimar   Afra    dan  haka bayan ya  gama  abinda ya kawoshi  yace ta shirya kayanta  daita zai wuce ran mahaifiyarta bai so ba  amman  haka ta hakura  ta barta dan bazata iya musawa alhaji realwan ba Suna isa gidan tun daga haraban gidan take ihun kiran sunan mufeeda  ....
itama  mufeeda ta kwaso da gudu da zahra   a daf da shigowa parlour'n suka haɗu suka rungume juna cike da murna ganin junansu suka karaso parlou'n suka zauna akan kujera suna maida numfashi mufida ta riko hannuta "afra  zo muje dakinmu ki ga yadda dady ya gyara mana an  canza mana  komai dake cikin dakinmu   ".
"Kai dan Allah ta fada tana mikewa  tsaye ba   dan taso ba     sai dan damuwar da mufeeda tayi daita dan jininsu ya hadu sosai ."

rike hannun Afra  mufeeda tayi  har suka shiga dakin sannan ta saki hannunta  "wooooowwww kai amman dakin ya qara kyau  sosai  anan zan zauna dan nazo kenan Bazan koma ba sai dai kai ziyara  "dan Allah da gaske kike "?"Allah kuwa take mufeeda ta rungumeta ajikinta suka faɗa saman katifa suna murna  komai na dakin milk colour ne Sai wordrobe da akayi musu mai  ruwan chocolate colour , suna rungume da juna zahra ta shigo d'akin "idan kun gama rungume juna ku gabatar da sallah kuzo muci abinci ". "okay suka hada baki gurin fadar haka sannan suka shiga bayi tare Afra  na tambayar mufida "ni kuwa ina wannan dan tsintuwar ban ganshi ba".? "Mummuy ta aikesa amman kinsansa  babu wasa bare bata lokaci yanzu  zaki gansa ya dawo "na so ace yana nan na  soma guma masa wahalalle  kawai ta karasa maganar tana kwashewa da dariya "dan Allah ki fitar harkarsa baki ga shi ko kallonki baya son yi ba"
"Kar ya kalleni mana Shima yasan abinda zai faru idan na kama shi yana kallona ". bayan sun gabatar da sallah suka fito  tare  dakin mumy ta shiga ta gaisheta  ta  fito rungume da Kisna  suka fara cin abinci jollof din shinkafa ce wacce taji kayan hadi  suna gama ci ta kwanta akan doguwar  kujera ta daura Kisna a ruwan cikinta  can bayan  kamar minti goma ta mike ta koma daki daga kwanciya  naunauyen bacci  ya ɗauketa  ."
Kamar yadda mumy ta fadawa muradi akan kar ya nuna kanshi hakan ce kuwa ta kasance duk inda zai ga Bature da garba baya kallonsu har ya kara girma yayi wayo basu san muradi yana gurin mumy ba a tunaninsu yana hannun yan fashi ....

Bayan shekara biyar

Sai ga sadiq  yazo  Lagos tare da mai gidansa  domin yin  aikin  panapiter a matuwaf   bayan ya gama abinda ya kawoshi    gidan   Alhaji Garba  ya shiga nema  ta hanyar  address dinsa daya amsa   dan tun a ilo yace idan ya gama abinda ya kawoshi  a gidan takwaransa   zai  sauka  idan ya huta sai ya nemi inda muradi yake , bai zo   da wata mummunar  shiga ko wani mugun yanayi ba tsab abunshi   ga tsananin kamarsa da mahaifinsa  daya  sake bayyana yatsun kafafunsa ne kawai na mahaifiyarsa sabanin muradi da komai na  haroon  ya dauko  sai bambanci halaiya kallo daya  matar Alhaji garba rabi tayi masa tasan dan haroon ne ta  tarbeshi cike da kulawa ta bashi abinci  bayan yaci yayi wanka.
lokacin da yaran gidan suka dawo daga makaranta  ta shiga nuna musu  sadiq   "ga takwaran babanku yazo  daga ilo yaran ma  sukayi murna sosai da  ganinsa   sai  dai akwana daya sadiq   ya raina  kanshi  dan fatata Alhaji garba  yayi masa  "me ya kawo ka  gurina ? kan sadiq a sunkuye yace "nazo wani aiki ne a matuwaf nace nazo mu gaisa daga nan na ...."dakata dakata banason jin dogon bayani   tashi ka bar min  gida kar na kara ganinka  a  kofar  gidana bare a cikin gidana dan halak ma yan fashi sunyi gaba dashi bare kai dan gaba da fatiha maza ka koma inda ka fito bama nemanka ko ka tafi gurin wannan ɗan iskan ubannaka hjy rabi tayi ta ƙoƙarin hana alhj garba abinda yake kokarin aikatawa amman yace sam bai yarda ba sadiq bazai kara ko second daya a gidansa ba ....
a kofar gida   sadiq ya hadu da Abubakar  yace "ina kuma zaka da jaka  ? ya   tambayesa   yana kallonsa goye da jaka    "zan koma inda na fito ne  ko kasan   gidan mama   salaha "? Abubakar ya  daga masa kai "yauwa na gode sosai dan Allah bari na baka wani  sako jakarsa ya bude ya ciro diary din mahaifiyarsu da yayi cel d'insa da takarda mai ruwan kasa "dan Allah ka bawa Aliyu "Abubakar yayi shiru yana tunanin waye Aliyu a gidan mumy salaha   ya gama  tunaninsa tsab bai gano wanda yake nufi ba "gaskiya bansan aliyu  a gidan ba "muradi fa dan ana kiransa da  muradin hajiya kayi "eh nasan muradi kana nufin kaninka ne muradi  ? sadiq yayi murmushi yace "eh dan allah ka taimakeni ka bashi wannan sakon naso zuwa da kaina amman ina jin tsoro kar naje can ma a koreni kamar yadda aka min nan yayi maganar a gaugauce "Abubakar ya girgiza masa kai "mumy bazata koreka ba ka bari zan kaika gidan "a'a na gode sosai ba sai naje ba zan je matuwaf nabi motar da muka zo dashi zuwa ilo ya mika masa ya wuce abubakar ya bi bayansa da kallo cike da jin tausayinsa kamar yayi kuka shi dai yana ganin muradi a gidan mumy salaha amman bai taba sanin dan kanin mahaifinsu bane sai yanzu ya dauka dan family mijinta ne , shiga cikin gidan yayi inda mahaifinsa ke bala'in da kunfar baki ",haba baba me yasa zaka koresa bayan jininka ne yanzu kasan inda zashi  daka koresa ..?"dan Allah kace ya dawo ya zauna anan tunda ma dan'uwansa na gidan mumy Alhaji garba yayi tsuru tsuru yana kallonsa cike da mamaki "yanzu sai  da salaha ta nemo yaron nan ai shi tunda akace ya bace yayi hamdala sun rage iri gyada kai yayi sannan ya shige dakinsa "gaskiya anya abinda baba yayi bai da kyau "kai ma karamin yaro kasan bai da kyau bareni na rasa me yasa babanku yake yin haka ? a ranar Abubakar yaje gidan mumy sai dai bai nemi muradi ba ya bawa mumy sakon sadiq sannan ya koro mata duk abinda mahaifinsu yayiwa Sadiq ta fashe da kuka tana cewa "wayyo Allah me yasa baka kawo min shi ba " sadiq din ne yaji tsoron zuwa tace karku koresa amman yace min matuf zashi d'ago kanta tayi sai ganin muradi tayi tsaye a gabanta idanunsa sunyi jawur alamu sun gama nuna mata yaji komai ta yafitoshi da hannunta sai dai zuciyarsa yazo wuya ya kasa daga kafafunsa ,hawaye ne ya shiga zubo masa yana son dan'uwansa shi kadai yake da yakinin yin rayuwa dashi tunda har wannan lokacin bashi da labarin mahaifiyarsu ko ma wanda yasan inda yake basu sani ba mumy ta mike ta kamo shi ta nufi ɗakinta dashi ta zaunar dashi tana karfafa masa gwiwa akan rayuwa "ka zama mutumin kirki muradi domin bawa wasu kunya kada dauki dabiar mahaifinka ka jajirce a rayuwa duk haroon ne ya jawo wa sadiq wannan rayuwa gashi bansan inda mahaifiyarku take ba wallahi da ni da kaina zan nemota kayi hakuri kaji kuka take shima yana yi ta mika masa sakon sadiq ya amsa ya kamkame ajikinsa yana cigaba da kuka yana mai tsanani tausayin dan'uwansa Gara shi yanzu mumy zata masa komai shi kuma tun farko shine yaki da yanzu suna tare ranar wuni yayi da dacin rai tare da kewar mahaifiyarsa da dan'uwansa "..

A  hankali  muradi  ya cigaba da

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login