Showing 111001 words to 114000 words out of 495987 words

Chapter 38 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt

sunanta  a tsanake  cike  da tausayawa  ,ta kasa amsawa  sannan ta kasa  d'ago  idanunta saboda hawayen  dake  cikinsu "duk  naji  abinda ya faru tsakaninki  da  haroon  amma  mai  zai hana kiyi hakuri  ki   bari  a cire cikin  so that daga  baya sai  a  san  yadda  za'a yi idan  ma  auren zaku yi sai  kuyi  ,kinsan mu  addininmu  ya  haramta mana    aure  da ciki "

  Kai  tsaye  girgiza  masa   kai  tayi alamun ta  sani   kafin  daga baya ta  soma  magana  cikin kuka  "nasan da haka Abdul  sai dai bazan iya zubar  da ciki ba  , dan  yarenmu   bama  zubar da  ciki  idan mutun yayi ganganci  zubarwa kuwa sunansa  gawa dan mutuwa  zai  yi ta  fadi haka   dan  kare  kanta   da  kuma  tsiratar da cikin  jikinta  dan  ita  tana  tsananin son  abinda   zata  haifa wa haroon  . bata  yi   auni  ba  taji saukar  zazzakar  muryarsa  a kausashe cike  da  tashin hankali  yana  cewa  "aikuwa  Ki  sawa  ranki  zaki mutu nan  kusa  dan wallahi  bazan   amshi  cikin  jikinki  ba   kije ki san yadda  zakiyi  dashi  ya k'arasa  maganar   a fusace  yana ƙoƙarin barin  gurin   tayi saurin shan  gabansa  tare da  riko  duka hannuwansa  hawaye  na gangaro mata  "haroon  karka  min haka   ni  bance  dole  sai ka  aureni  ba  amman  ka amshi  cikin jikina a matsayin  d'anka  a  zuciye  ya fixge hannunsa  daga  cikin nata   yana  nunata da ɗan   yatsansa  alamun gargadi   , abdul   ya matso  kusa  dashi kamar  yayi kuka  yake duban haroon  dan ba karamin tausayawa dicter  yayi  ba  , babu   yadda   bai yi da haroon  akan  ya  hakura ya amshi  cikin  ba  hakan   ba zai zama da  wata matsala  ba  hasalima babu  sisinsa da zai kashe  akan  cikin  amman  haroon yaki  yarda  yace "shi bai tashi haihuwa  da kowace mace  ba  koda kuwa da  macen  da zuciyarsa ke so  ce  bare  ita  da bai taɓa  jin digon sonta acikin   ransa ba .."

Tun  da  ya soma  magana  idanunta ke  kansa   tana  ci-gaba da  zubar  da  hawayen  bakinciki  "me  ta rasa da haroon  ya  kasa fuskantar lamarinta"?" ta  haɗa  komai da duk wani  cikakken namiji zai bukata  daga cikakkiyar macen  data amsa sunanta  ,kasa  hakura tayi  ta  sake matsowa garesa  cikin  narke  fuska  ta  durkushe a gabansa  nan  fa hankalin  mutane ya karkata  garesu  suka zuba musu ido  suna kallonsu   , cikin  rawar   murya  take  magana jikinta   na  rawa   "haroon  zuciyar  dicter  ta makance   akanka, zuciyarta  bata   taɓa tsintar  kanta  cikin yanayi  irin  wannan ba , ka  tausaya  mata karka barta   babu  abinda zuciyata  take  buƙata  kamar  ta  mallakeka ,
zanyi  komai  akanka  dan   bana  son  yadda   soyayyarka  ta  ladabtar dani   ta  labdatar  da abinda  ke cikina , idan  zuciyarka  ta makance akan  kiyayyarta   bai  kamata  idanunka su makance   akan  tilon  dan d'an da   zaka  fara  samu a  duniya   bayan dogon   lokacin   daka ɗauka  kana  tarayya da mata  kala dabam dabam   cikinsu  babu  wacce  ta dauki cikinka bare  har  tayi niyyar haifa  maka   sai  ni  da kake  jin tsanata fiyye da kowace  mace a duniya   , idaniyana  sun makance  akanka  haroon  duk  da kiyayyarka  gareni ammna  har yanzu  rayuwata  na kaunarka da  tillon  danka ko yarka  dana  fi  so  fiyye da komai  a rayuwata  kai muslimi ne na zauna tare da  muslimai  suna da tawakalli   da  yarda  da  hukunci Allah  komai suna daukarsa a matsayin kaddama ina rokonka  ka  yarda  da  kaddarar  cikin nan mu barshi  ya rayu  da........"
" Enough   dicter  ya katseta  a  matukar  tsawace    yana  mata gargadi   da  idanunshi,  gabad'aya  yanayinsa  ya canza    hatta  kwayar idanunsa   sun canza launi  ji yake kamar ya shaketa  ta  mutu ya huta  "mai  yasa  kike da taurin kai da nacin bala'in ? Shin  ko  kinsan duk wannan abinda kike yi baya  sauka  akan  zuciyata  bare  naji shi a jikina? ciki  dai  nawa ne ko  ?  Tayi saurin girgiza masa kai tana marairaice fuska " to  nace  miki   banaso  bana  bukata  ki  zubar  ko  kuma ki zama  uwarsa  da  ubansa  wannan kalmar itace silar  bugawar  zuciyarta  "meye  farinciki ka  a rayuwa haroon da zaka nemi wulakanta  jininka ? "Ina tabbatar maka muddin ka wulakanta wannan cikin bazakayi farinciki a rayuwarka ba saboda baka cancanci samun haihuwa arayuwarka   bayan ka wulakanta ya'ya bilaadadin "ki  min shiru stupid  idan  ba haka  ba zan  daga miki hankali zan  baki   mamaki  ina ruwanki  da ko duka ya'ya na  wulakanta  ?  ganin suna maidawa juna  magana cikin tsananin fushi da zafin zuciya    yasa  Abdul  ya  matso ya  shiga  tsakaninsu  yana bashi  hakuri   da ƙoƙarin shawo  kansa  amman taurin  kai  irin na zarma ya  matsowa  haroon  yaki  fahimtar  abokinsa  haka  Abdul   ya hakura ba  don  rashin  yayi masa  dadi  ba ,  suna kallonsa  ya  tsaida mai mashin  ya  haye ya barsu  tsaye  jigun jigun tamkar  waɗan da aka yiwa  mutuwa , Abdul  ya  dinga  kwantar mata da  hankali  da bata  tabbacin  zai shawo mata  kanshi a karshe ma  zai  dawo gareta nan kusa , da zantuttukan masu  sanyi  ya samu ya dinga   kwantar  mata da hankali  ta  nufi gidansu  zuciyarta  na rawa  ..."

    Daren   ranar   dicter  bata  runtsa  ba   babu abinda  kwakwalurwarta ke  yi  sai  tunanin nemawa  kanta  mafuta  ,kanta   kamar zai  tsage akan tunani gabad'aya  ta rasa abinda ke  mata  dadi  damuwa ta  samu  kyawawan mazauni  a cikin zuciyarta  idanuwanta kuwa  sun kankance saboda  tsabar  kuka har lokacin  ma hawayen idanunta  yaki  tsayawa akan  kyawawar fuskarta , ta  kai  hannu ta goge hawayen  a lokacin da wasu  zafafan hawaye suka  zubo mata , kuma har  lokacin bataji zuciyarta   ta amince mata  da  zubar da cikin jikinta ba   , har  goshin asuba  bata  samu   damar   runtsawa   ba, washegari    taki    fitowa  har kusan karfe   biyu   jin shiru yasa mahaifiyarta  ta shigo d'akin  ta isketa kwance  shiru  ta lula duniyar tunani , hankalinta a tashe   ta  karaso  gareta ta   tambaye   ko lafiya bata  fito  ba  tace "kanta ke  mata   ciwo "shine zaki  kunshe  kanki a daki  dan  rashin  sanin ciwon kai ,maza  ki  tashi akai ki hospital  ta gyada mata  kai  tare da mikewa  zaune   ita  kuma  ta  fito daga  dakin , bayan mahaifiyata  ta  fita   daga   d'akin   komawa tayi ta kwanta   tana  fidda  numfashi  sama sama  yayinda   duka  hannuta  ke kan  cikinta   da taji yana mata  kugi  alamun  jin yunwa  ranar  haka ta yini da   zazzafan   zazzaɓi da  yunwa   ajikinta  ko  falo   bata  fito  ba mahaifiyarta  ta  sake  shigowa d'akin  wanda   lokacin  tare  suka shigo da likita ta  nuna  masa inda take kwance ,  ya ajiye jakar kayan  aikinsa ya soma dubata  tare da yi mata allurai  da rubuta mata magani  dan  bayi  tunanin  aunata  ba  ya fita  ...."

Tun   daga   ranar dicter   bata  kara  samun  lafiya  ba   tayi   bankwana da farinciki   duk  abinda  taci  sai ya dawo  ga miyo laulayi  dai  ya  tasa gaba  sai  ɗaukar  hutu  tayi a  gurin  aikinta   Abdul  ma bai  zauna  a garin ba  ya tattara ya  kama  gabansa  saboda gudun abinda  zai  biyo baya, sai da  cikin dicter  yayi wata biyar  cikin na shida sannan  mahaifiyarta ta fahimci  ciki gareta tashin  farko tayi murna dan  su a yarensu bawani abu  bane  dan mace tayi ciki , amman  jin wai mai cikin  yaki  amsa kuma muslimi  ne  yasa hankalinta  yayi  bala'in tashi  ta  dinga zaginta tare   da   kiran  zata gurbata  musu zuri'a da muslinci , haka ma y'an'uwanta  sanda  suka ji  labari  suka hau bala'in tare da     zarta hukunci  akanta ko a zubar da cikin ko   tana  haifar abinda ke cikinta  ta bar musu gidan  da  yaron  basa bukatarsa  cikin family dinsu  hakan  ya sake haddasawa  dicter  shiga damuwa  kullum da tunanin  take  kwana take tashi  tunda ema yasan da batun cikin kullum  kafar  na gidan yana  surfawa dicter tujara  iri iri  yaki  yarda a daidaita komai  burinsa ta yarda a cire ciki  ko kuma da  zarar ta haihu ta bar musu gida "hawayen  idanunta sunki  tsayawa kalma  daya ce dai  ke  fitowa daga bakinta  "kuyi  hakuri ku bar min cikina da zarar na haifa na yarda zan barku "wannan  kalmar  ke karyar  da zuciya mumy tayi  kukan zuci  babu halin yin magana dan  sai tayi  kamar zata yarda  da  zaman dicter  da cikin jikinta sai  ema ya sake harzuka ya dinga  zugeta  tare da sauke  mata kwando maseefa  da bakaken kalamai  ya nuna mata  itace ke  daure mata gindi  ,fita  yayi daga d'akin  cikin bacin rai mumy ta bishi tana masa magana cikin harshensu "me kake son nayi  ema ? "Ni kaina ba farinciki nake da wannan cikin ba "to me yasa kike   zuwa  kina  tarewa a gurinta kina nuna tausayawarki gareta  alhalin  kinsan  babban  abun kunya  ta aikatawa danginmu   idan kin  yarda da zamanta mufa bazamu lamunta ba gara tun  wuri musan abun  yi ki zaba ko mu ko ita?  mumy tayi  shiru zuciyarta na zafi duk  maganarsu  tamkar a cikin kunne dicter suke yi sakamakon biyo bayansu datayi domin sanin  matakin da zasu sake dauka akanta  "daga yau karki sake  zuwa inda take matsawar kina son mu zauna lafiya,  mumy ta sake  yin shiru tana kallonsa "shirunki  ma  kawai amsa ne ya sa kai ya fita ya barta da ciwon zuciya .

tun  daga  ranar mumy bata sake shigowa  inda dicter take ba sai dai hankalinta  na kanta  tana tura mai aikinsu  ta Kai mata abinci tana lura da  duk wani motsinta rashin shigowar mumy  yasa   zuciyar  dicter ta fara  ciwo saboda  kadaici yayi mata  yawa ,  domin    dauke kafar da mumy tayi daga shigowa dakinta babban tashin hankali ne  gashi  bata   samun  mai kwantar mata da hankali ba , kullum cikin damuwa take .
da  wani yammaci ta kunshe kanta  a tsakankanin cinyoyinta tana kuka mara sauti mai tattare da  bakinciki halin da take ciki  mussaman  yadda Haroon  yaki  abinda  yake  cikinta bata  san yadda zatayi da rayuwarta da  cikin  jikinta  ba  tana  jin  kamar ta  zubar da cikin  ta zauna da yanuwanta  lafiya ta huta da balai  sai dai  wankakkiyar  zuciyarta  na kwabarta  da aikata haka ,a lokacin ta sake  yin  baki ta Rame gabadaya ta fita  haiyacinta saboda rashin samun natsuwar  zuciya  da kwanciyar hankali , ita kanta mumy  zuwa lokacin  ta soma nuna  tausayin  diyarta  ta damu  sosai da ramar datayi  ga ciki gabadaya damuwa ta aureta kana ganinta kasan tana cikin damuwa  dan dai bata son nunawa ne kada  manya  yayanta  su  dauka da gaske  tana goyon bayan dicter ne, kuka take sosai tun daga lokacin da cikinta ya tsufa bala'in ema da sauran yan'uwansa ya karu  kuma a lokacin ta  hakikancewa kanta yanuwanta baxasu amince da zamanta da abinda ke  cikinta  ba  a  gidan  sai  dai ta kudurcewa  kanta bazata rabu da cikinta ba ,zata  haifa kuma zata rayu dashi  ko bola ne taje su rayu amman bazata taba biye musu ba bare ta wulakanta abinda zata haifa , dan bata sani ba ko cikin jikinta kadai zata mallaka a rayuwata  ."

sannu  a hankali ta cigaba  da  renon cikinta har  sanda  ta haihuwa ta samu  d'a namiji  kyakkyawan gaske  wanda  yaci  sunan abubakar  wato sunan yayan  haroon  tana kiransa  da  sadik  , limamin    unguwar su ta samu  ta koro masa bayanin  cewar uban yaron  muslimi ne dan haka  tana  buƙatar a saka masa sunan Muslunci  bayan limamin ya  gama  jin  komai  ya tausayawa  rayuwarta  da yaron  sannan ya bukaci  sunan  da take buƙata   tare  da karanto mata  sunayen maza a Muslunci  har yazo kan Abubakar  sadiq nan ta tuna  haroon ya taba faɗa  mata  yana da yaya Abubakar , a  hankali ta cigaba  da  bawa yaronta kulawa  sai  dai  kullum da  abinda  take gani daga  y'an'uwanta  wanda bata  tsamaci  hakan daga  gare su ba, ta ɗauka   kaunar dake tsakaninta  dasu  zatasa zuciyarsu  tayi rauni su kaunaci  abinda ta haifa sai  gashi  a dalilin tilon d'anta  sun   sake tsanarta  da nuna mata  ita din  ba kowa bace  garesu  gashi shima  uban  ɗan ya nuna  duk duniya bashi da  makiyiyar  data wuceta  ,tun mahaifiyarta najin  haushin  yaron da bai ɗauko   komai nata  ba  sai  na ubansa   ta dawo  ta soma  sausauta mata  da  fahimtar kowa da irin tashi  qaddarar ,bazata rabu   da tilon diyarta ba  amman dole a fitar da  yaron daga gidan dan ganinsa  nasata  jin bakinciki  mara misaltuwa  kuma hakan na hura wutan bala'in a gidan .

tana tsakiyar katifarta  a zaune  tana bawa  yaronta ɗan  wata hudu  zuwa  biyar  nono, yayanta  Emanuel  da mahaifiyarta  suka shigo d'akin  ta d'ago kanta a hankali  ta  zuba musu ido  tana jiran taji abinda ya  shigo  dasu " yau ne  watanni    dana  baki suka   cika tun bayan haihuwar ki   ki ɗauki  wannan  yaron  ki kaiwa ubansa  ki dawo mu cigaba  da rayuwarmu kamar  yadda muka gabatar  a tun farko  idan kuma  kinki  amincewa da  tsarinmu sai  ki tattara  ki bar mana gida ki bi ubansa  dan  ba zamu  zauna tare da dan muslimi   kuma wanda ya nuna  baya  qaunarki  , bancin  ke ƙatuwar wawiya  ce ta yaya zaki shayar da  wannan dan  bayan ubansa   yaki amincewa dashi  sannan   ya  nuna rashin  kulawarsa  gareki".
"yaya  zanyi da rayuwata  "?ta  fada cikin  raunin murya  "ku min uzuri dan Allah  ni kaina ban tsamaci  irin wannan rayuwar ba ,sai dai kusani   ko  na  kai masa yaron  nan  babu abinda zai  yi  dashi tunda ya nuna  baya bukatarsa a rayuwarsa   ,sannan meye  ribar na  bayar da tilon  d'ana na dawo na cigaba  da rayuwa  tare daku batare  dashi ba? " ina son dana  Kuma duk runtsi  zan rayu dashi koda  kuwa zanyi rayuwa akan   bola ne, ina rokonku   kada ku bari wannan  al'amari ya  farraka  tsakaninmu ,ba kowace  uwa ce zata iya rayuwa  babu d'anta ba dukkaninku  iyaye ne ku misalta  haka akan kanku , "mai yasa zaku zama  makiyana akan abinda  bai kai ya kawo ba "? "Mommy  ke fa uwace  kin fi kowa sanin yadda  ya'ya suke a zukatan  iyayensu ke kanki  bazaki so rabuwarki   dani ba, Ki duba  kiga yadda kike jina  aranki ,yadda kike mutuwar  sona a zuciyarki   yadda kike ji akaina haka  nake jin soyayyar   dana  araina koma  nace  fiyye da irin son da  kike min saboda ni  na samu gatan da soyayyar iyayena wanda  d'ana  ya  kasa samu daga  gurin mahaifinsa gabad'aya  jikin mommy yayi  sanyi  ta dukar da kanta   sai hawaye sharrrrrrr sharrrrrrr ..........
"ema  ya kalleta a fusace  "bafa  zamu cigaba   da zama dake  da wannan dan ba  , ai da ɗan iskan yaron da yayi miki ciki bai  gudu   ya bar garin ba  da sai yasan yayiwa  miki ciki   dan tuni zan sa bindigata na  harbe    shege  ko ya  kai wa uwarsa dan  ta  goya ,   sati   daya   na   baki ki san abin  yi   dan  mu fiki  shiga  kunci da bakinciki  wannan abun kunyar da kika   yi  wai ki rasa wanda  zaki yarda kiyiwa ciki  sai  muslimi  duk fadin garin nan   kin  bani kunya  dicter  banyi exepecting  haka ba     yana gama  fadar  haka ya juya fuuuuuuuuu  ya fice daga  d'akin sosai take  kuka sai  dai  har lokacin zuciyarta   batayi  nadamar   haihuwarta  ba  mumy ta zauna kusa daita ranta duk a jagule sai dai ta rasa me zata fada mata .."

Bayan kwana biyar din da ema ya bata ta soma shirya kayan Sadiq  a cikin jaka tana kukan zuci tana tunanin sauran kwana biyu kwanakin da ƴaƴanta ya bata da  inda zata ga haroon  yayinda   mumy  ke rakube a gefenta  rungume da sadiq tana kukan zuci dana zahiri ta ya zata rayu batare da diyarta ba dicter na cikin hada kayanta ema ya bude dakin ya hankado labule ya shigo mumy na ganinsa tayi saurin ajiye Sadiq akan katifa jikinta na rawa suka zuba masa ido suna kallonsa gabansu na faduwa balle da suka ga ya tokare a bakin kofa sai huci yake, addu'a dicter  ta  soma yi acikin zuciyarta "fatan  baki manta ba jibi  ne kwanankinki  zai cika a gidan nan ki tattara ki bar mana gida dan baxaki reni Dan musmulimi a gidan ubanmu ba idan kuma kinki zaki nacewa zaman gidan nan   zamu  kawar  dake da  wannan  yaron mu huta take mumy ta tsure tana cigaba da kallonsa "kisa  kake  nufi ema ko me ?
Ya watsa mata idanu "kisa kuwa ko zaki hana ne ? Ta girgiza masa kai  alamun aa"babu abinda ya dace daita sai mutuwa  ,take dicter tayi luuuuu zata fadi akan Sadiq mumy tayi saurin tallabota abun haushi suma ta so tayi amman suman yaki zuwa dan haka ta zuba masa ido cikin wata irin gigitan  jin abinda yace  zuciyarta na dokawa  kuka ya kufce mata "yaya yanzu har munzo lokacin da zaka iya kasheni akan wannan matsalar?
a fusace ya d'aga mata hannu "dan ubanki  akwai  abinda yafi dace wa dake bayan mutuwa  ? " idan mun kashe danki  zaki dangwama kina ganin bakinmu idan mun kasheki mun bar danki  zai rayu tare damu abinda  bazamu so ba kenan kinga gara ku tafi gabadaya  tunda kin zabi rayuwa dashi sai  lokacin  mumy ta sanya  baki cikin tsinkewar zuciya da tsoro  "haba  ema bai  dace kana fada mata  haka ba idan kayi haka kayi ..
Yayi saurin katse mumy "bazamu fa bar wannan munafukar ba,sai dai  ta zabi daya cikin biyu ta kaiwa mai da dansa ko suyi  mutuwar kasko mumy ta zaro ido tana dubansa jikinta na rawa  hawaye ya zubowa mumy a lokacin da dicter  ta zube gabanta tana kuka irin kuka a kausashe "kada ku min haka ko addinin muslinci babu inda akace zaa kashe mutun dan yayi ciki da Christan ,dan Allah   karkayi haka wannan  jahilce ne kai da zaka tsayawa rayuwata akan dana daya zamo qaddara a rayuwata kai ne .... "dakata ya daga mata hannu kenan kin zabi muslinci akan addininki tunda har kina ganin a muslinci bazaa iya yin miki  haka ba  ? "Tabbas na zabi  muslinci akan addinina  kuma ina daf da amsa a fusace yace "ki min shiru wawiya makaryaciya kawai ki fita idona kafin na karyaki dan ubanki kin dade  baki amshi muslinci ba , kuka sosai take na bakinciki  wannan tsanar da yanuwanta suka mata "kada ka  cutar Dani Kai danuwana ne idan kayi haka Allah bazai barka ba haka dicter ta dinga furta masa magana cikin muryar kuka tana ajiya magana   zai dauka "anya kuwa yaya kana da digon imani a zuciyarka ?"kana tsoron Allah kuwa  ?"idan kika

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login