Showing 75001 words to 78000 words out of 495987 words

Chapter 26 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt

ɓacin rai ne , karkayiwa rayuwar aurenku nakasu  alhalin kuna bukatar juna ,ka tsaya ka duba rayuwar ƴaƴansu uwar wani da ɗan wani sai Allah babu wanda zai iya kula dasu Aryan kamar kisna, ka barta a gindin ƴaƴanta da ita kadai suka saba  sannan ina kake tunanin zata  idan ka saketa tunda kasan abinda dady yace mata kayi hakuri dan Allah  ta tarkashe maganar kamar zata yi kuka ...."

d'akin ya dauki shiru na wani  lokaci  sannan sautin muryar kisna ya karade dakin " aunty zee ki daina bashi hakuri dan girman Allah   ki bar shi yayi  duk abinda zuciyarsa  ta yanke masa  akaina  ko dady da mommy sun ki amsata amatsayinsu na iyayena  zan bi duniya ,zan kwashe  yarana mubi duniya  tare dan bazan bar ko daya ba  ya sake d'agowa   a  matukar fusace yana kallonta da jajayen idanunshi da suka canza kala  "da wasu yaran zaki bi duniya  ?  Yayi maganar kamar zai cinye ta "idan zaki bi duniya ki bi duniya  ke kadai kar ma ki tsaya  a iya duniyar  mutane  ki zarce zuwa wata  duniyar  daban i dont fucking care  amman ban da ya'ya na ...." ya karasa maganar a zuciye yana baro inda yake ya iso gabanta ya tsaya suna fuskantar juna "idan kin shirya yawon duniya ki tafi ke kadai karki sake ambato ya'yana a ciki  okay idan ba haka ba zan kasheki da kai kaina ya karashe maganar yana nuna mata yadda zai yi daita ".

  a hassale tace "lokacin dana yi d'awainiyya da cikinsu kana ina "?  ta kai hannuta  qirjinshi tana nuna shi jijiyon wuyanta  na mikewa  sabida tsananin  tashin hankali da jin dacin maganarsa " kana ina  nace ? " kana  ina na  ɗauki tsawon kwanaki    ina nakudarsu  sannan na haifeshi kana ina "? "kasan yadda ake daukar ciki ko kasan yadda ake nakuda bare ka faɗa min magana   akan ya'yana   ka bani amsa tambayarka nake ? ta dinga zuba masa magana tana nuna qirjinsa tare da  turesa tamkar mahaukaciya sabuwar kamu shi kuma yana ja baya ganin kamar ta soma fita haiyacinta  yasa a  zuciye  ya damki kafad'unta ya haɗeta da bango  dakin "shut up kisna !!!! I said shut up or  else I will get you lost on second are you insane ? ya cigaba da  magana cikin zafin rai  "ko kina hauka ne kike ture ni  " ?"Ko  kin  soma shaye shaye ne  ko kuma  tsohon haukan  rashin mutuncinki ne ya motsa "? " alright ai nasan bazaki taba  canzawa ba dan idan kayi shekara dari baka haɗu da mutun ba duk ranar daka haɗu dashi karka tambayi halinsa dan halinsa na nan  bai canza ba , da wannan halin  kike tunani zaki  mallaki zuciyar Aliyu never in history? " Aliyu yafi karfinki yayi miki nisa da.....

"Papa Me yasa kake sa mommy  Kuka  ?  Suka jiyo sautin Muryar aryan yana kuka har da shesheka " kullum kana sa mommy  kuka bana sonka tunda kana sa mommy kuka  daga yau kai ba papa dina  bane, babu ni  babu kai ".ya riko hannun aryan da niyyar rungumeshi yaron ya  fixge  hannunsa ya karasa  jikin kisna  yana goge mata hawaye "stop crying  mommy ,I will  tell Grandma to punish him wasu hawaye suka zobo mata ya sake goge mata ta karasa ta dauki areef  ta saba shi a kafad'anta ta rike  hannun aryan suka bar d'akin ."

  "kaga abinda kake kokarin haddasawa  ko ?" wannan karamin   yaron   da bai san  meye damuwa ba amman yau   saboda ganin uwarsa cikin damu...........
"ya damu ko kuma ana son gurbata min tunanin yaro ya dauka ni din mugu ne "dan girman Allah kayi hakuri ya Aliyu komai ya wuce karka sake tada maganar  nan plz numfashi ya sauke jikinsa yayi  matukar yin sanyi saboda ganin yadda aryan ya nuna reaction dinsa akan kisna    ya juya  ya fita zuwa haraban gidan kanshi kamar zai kama da wuta nasir ya dake zaune ya kalli samir "tashi mu bishi mu shawo kanshi , Samir  ya masa banza ganin haka yasa  nasir ya  mike ya  fita,Aliyu  yana tsaye hannunsa daya dafe da goshinsa  dayan hannunsa  yana cikin aljihunsa nasir  ya karaso   ya rike hannunsa ya nufi lambun gidan  dashi  batare da yace masa uffan ba shima ya bishi a baya har suka shiga ya zaunar dashi ya koma   ya dauko ruwa mai dan sanyi  ya ɓalle murfi ya mika masa "ka sha kaji sanyi a hankali  ya amsa ya  kafa bakinsa a bakin goran bai sauke ba sai daya shanye tasssss  .
Yana  ajiye goron nasir  ya fara magana cikin fushi  ta inda yake shiga bata nan yake fita ba "karka ɗauka ko na shigarwa kisna ne a'a ina fada maka gaskiya ne  a matsayina na d'anuwanka  kuma abokinka saboda  bai dace ba ko wata kayiwa haka  ba kisna ba zan tsaya tsayin  daka naga na faɗa maka gaskiya shima Samir sam bai ji dadin abinda kayi ba   ya  dai  kasa saka  bakinsa ne   bisa wani dalili nashi  ,ko  baka duba darajan kowa ba ka duba Samir mutumin da rayuwarsa ne kawai bazai iya baka ba ,mutumin da kai da kanka ka sha fada min yadda kuka yi rayuwa tare haba muradi ai ko mutuwa tana jin kunyar  idon iyaye ,ya'yan nan fa ƴaƴanta ne bazata so abinda zai cutar dasu ba sannan duk sonka dasu bazaka Kai ta ba, nasir ya dade yana masa magana  jikin Aliyu ya sake yin sanyi sai lokacin ya fara tunanin yanayin da Samir ya shiga a lokacin da yake wa kisna tujara "kenan haushinsa Samir   yaji  ko me  .."? Yayiwa kansa tmbayar yana duban nasir ƙwaƙwalwarsa na sake shiga caji "Idan kuwa haushinsa Samir yaji lallai jini ba karya ba "amman har an zo lokacin da samir zai yi fushi atsakaninsa da kisna ?    sun dade zaune   a lambu  nasir na nusar da Aliyu gaskiya bai dai kula sa ba haka bai ce masa ya hakura ba illa iskan da yake furzarwa .."


Misalin ƙarfe biyar  mommy ta shigo parloun  aunty zee ce da safiyya suna zaune " assalamu alaikum ta furta a hankali tana karasa shigowa gabad'aya suka maida hankalinsu gareta "wa'alaiki salam tare da mikewa suka amshi  laidodi dake  rike a hannunta ta zauna akan kujera "ya Allah ta  furta a hankali ina waɗan sojojin  suke ban ji motsinsu ba"?
Safiyya da aunty zee suka kalli juna sannan aunty zee tace "suna sama tare da mammansu bari na kawo miki ruwa ki sha sai naje na dauko miki su ta karasa maganar tana shiga Kitchen bayan kamar second biyar ta fito hannuta rike da jug da glass cup ta tsiyaya ruwa  ta mika mata ta ajiye sauran a saman table  sannan ta juya ta hau sama mommy ta kalli safiyya "ina nasir ko  suna  bangaren Samir ne ko suna  lambu  "?
"Eh suna lambu "ta bata amsa da haka  suna zaune aunty Zee ta dawo "mumy bacci suke daga su har mammansu ta fadi haka ne dan kar mommy ta d'ago komai "bacci a daidai wannan lokacin ki koma ki tasota  ga waya nan na siyo mata   ta bude ladar data shigo dashi ta mikawa aunty zee wayar  "gashi nan ki   tasheta  ki bata "kai mommy gaskiya ta gode  kisna zata dawo online  kenan ? "Gaskiya wayar tayi kyau sosai " dubu ɗari biyar   kenan a kudinmu na nigeria zaro ido aunty zee tayi "haka waya yake da tsada anan ?"sosai kuwa ai wayoyi sunfi sauki a Nigeria nan dai  aunty zee ta dinga jan mumy da hira daga karshe nasir ya kira safiyya a waya tayi musu sallama ta wuce aunty zeey ta shiga Kitchen domin  daura abincin dare .."

Haka nan jikin mommy ya dinga bata akwai abinda ya faru a gidan da bata nan dan har kusan takwas din dare bata ga yaran ba haka bata ga kisna ba hankalinta yaki kwanciya gashi ita ta kalli abincin da  aunty zee ta kawo mata bata jin zata iya sanyawa cikin komai batare da ta daura idanunta akan jikokinta mafi soyuwa acikin ranta ba ,ta mike ta sanya silifas ta fito daga d'akin ta karasa bakin kofar dakinsu har zata tura sai tayi tunanin watakilla Aliyu yana ciki   tayi knowking  tare da sallama ......"

Aliyu ne ya taso sanye da jallabiya  dan maroko  kalar dark blue jallabiyar tayi masa kyau sosai abunka ga fari sol    ya bude kofar ganin mommy  tsaye  ya sha jinin jikinsa sai dai yayi kokarin sanyawa jikinsa jarunta cike da girmamawa yace "barka da dare  mommy , kina bukatar  wani abu ne "?Girgiza masa kai tayi kana tace "yaran nan  nazo dubawa tunda na dawo daga kasuwa ban sanya idanuna akansu ba daga su har uwarsu shiru yayi dan shi kansa baya son mommy tasan abinda ya faru ,idan ya hanata ganinsu zata fahimci wani abu idan ya barta ta ga hannun areef hankalinta zai iya tashi fiyye dana yanzu  duk da bawani ciwo bane ,hannu dai yayi sanyi ne saboda shock din daya samu , matsawa yayi gefe ya bata hanya ta shigo d'akin akan gado ta hago su kwance lullu'be cikin bargo kisna na zaune a gefensu jingine da gado ta tafka tagumi  tana ganin mommy ta sauko tana wayancewa ",mommy kiyi hakuri kin jini shiru ko wallahi tunda kika fita kaina ke ciwo shine na kwanta har yanzu ma ban daina jin ciwon kan ba momy  ta zuba mata ido tana nazarinta sannan ta karasa gurin yaran ta shafa kansu  tayi kasa da hannuwanta zuwa kirjinsu taji numfashinsu na sauka yadda ya kamata   ta rankwafo  ta sunbuci goshinsu ta dawo ga kisna "kiyi kokari kiga likita kada ki tsaya gida shan magani a tare kisna da Aliyu suka d'ago suka kalli juna qirjinsu na mahaukacin bugawa da wani sauri mommy kuwa tana gama magana tayi musu sai da safe ta fita Aliyu ya kulle kofar ya  hau saman katifa ya yi rigingine rungume da hannuwansa duka a qirji yana tunanin maganar mumy da alamun ta dauka ko ciki ke ga kisna ..?

    Har kusan dayan dare kisna bata runtsa ba tana kwance kusa da ya'yanta shima ba  runtsawa yayi ba tunani ne ya sha kanshi ta kai hannu ta janyo laidar da aunty zee ta shigo mata dashi d'azu tana dubawa wasu zafafan hawaye ne suka zo mata "uwa kenan "hakika duk wanda ya rasa uwa yayi kuka tasan  ta siya mata wayar ne  a matsayinta na yarta da kuma kwantar mata da hankali dan ta zauna da Aliyu gashi wanda ake wa dan shi yaki kwantar da kai su zauna lafiya ta mike dan saka wayar a caji   motsin laidar ya tadda areef ya Mike zaune Aliyu yayi saurin kamoshi jikinsa  ya rungume shi "zaka ci abinci ne?Yaron ya girgiza masa  kai yana cewa  ",papa tea "
da sauri ya sauko yana ƙoƙarin fita kisna ta rigashi fita  dole ya dawo ya zauna rike dashi bata dade ba ta dawo hannunta rike da cup din tea ta amshesa a hannun Aliyu ta soma bashi  can shima Aryan ya farka  ta dauko shi ta bashi sauran tea din da areef ya sha  ta kwantar dashi  ta shiga bayi dan bata jin zata iya runtsawa ta d'auro alwala ta fito wanda zuwa lokacin ya kwantar da areef a kusa da aryan sai dai idanunsu biyu yana lallabasu dan su koma bacci   .."

Tana zaune byn ta idar da sallah ta fashe da kuka yaranta dake kwance suka sauko a gigice  suka karaso gareta suka rungumeta kuka take suma suna    kuka   kamar ana zarar ransu kuka yaran suke sosai saboda ganin halin da take ciki gashi dai    basu da cikakken wayon da zasu ce ga dalilin kukanta sai dai suna jin zafin halin kunci da mahaifiyarsu take ciki a hankali ta rungumesu ajikinta tana ci-gaba da kuka "Allah kasa papa ya daina saka mommy kuka  kasa ya bata farinciki  , ki daina kuka kinji  mommy duk aryan yake magana shi areef ganin mamansa da d'an'uwansa na kuka ne  yasashi kuka "na gode d'ana  na daina kuka  kaji babana Allah yayi muku albarka na gode muku ,kuma na godewa  Allah daya azurtani da samu ya'ya irinku masu tausayi Allah  yayi muku albarka ta karasa maganar tana shafa kansu ....."

Mmn sudais
[7/19, 5:32 PM] +234 803 631 5951: 💗💗💗💗💗💗
  CUTAR DA KAI
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

Free page 13

~TRUE LIFE STORY~

*PAID BOOK*

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim

"Wannan  littafin na kudi ne  ,mai bukata karanta shi  zai  tura 500 ta wannan   account number  din  1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an  tura sai a turawa wannan number alert  +234 803 238 4602   domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi  sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne .  "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi  za'a iya tuntu'bar  Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos  lace da kamfala  ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da  chiganvy, volyal lace  duk akan farashi mai sauki ,ga mai  bukatar  siyan ɗaya ko sari  yayi magana ta wannan number 08059623096,yauwa har ma da agwalumar cotonou mai dan Karan zaki muna turawa kowani gari ...🥰🥰

    Muryarta   a  dake tace "bawan  Allah  kayi hakuri ni  din  matar aure ce  fa" wani irin kallon raunin wayo   yayi  mata sannan ya   gyara  tsayuwarsa tare  da zube hannuwansa  duka cikin aljihun wandonsa yana wata   irin   dariya har ya neman  d'aga  murya , cike  da  matsanancin tsoro  ta matsa baya da sauri  haɗe da rike hannun  d'anta  gam  dan ba karamin tsoro ya bata ba , a zahiri ake iya  hango  tsananin tashin hankalinta  waige waige ta soma yi  tana neman  hanyar  guduwa ciki  zolaya  yace "dakata ! dakata!!  mana Karki  gudu  dan  duk inda  kika shiga a kasar nan wallahi   sai na zakuloki  matsawar  kina cikin garin  nan  na mallakawa zuciyata ke  ".Yayi maganar hankalinsa kwance yana nuna ta da ɗan yatsansa yayinda idanunshi ke tsaye kyam akanta yana mata wani irin kallo  yana cigaba da dariyar da yake dan shi karya ya dauki maganarta ...

"a matukar tsoroce ta dubeshi   kamar  zatayi kuka tace   "dan  Allah malam ka daina  kallona haka  wallahil azim  ni matar aure ce har ma da yara biyu ..." ta karasa maganar idanunta na ciccikowa da ruwan hawaye .
Cak  dariyar dake kwance akan fuskarshi ta 'bace  zuwa mummunar ɓacin rai  sannan  yayi  shiru yana kare mata  kallo sama da kasa  zuciyarsa na wani irin tsalle da bugawa ,  sam bazakace  matar aure bace  komai na jikinta  irin na yammata ne  hatta shigar jikinta  yammata dayawa  suna yi irinta  yayi maganar acikin  ranshi "oh my goodness  ya furta a fili  yana  dafe goshinsa  ,"amman ko waye wannan mutumin  daya aureki  ya cuceni ya cuci rayuwata  ya gama dani  kalar  matar dana dade ina  nema na  aura wayyo Allah  naga samu naga rashi  tawa ta sameni  a fili  yayi maganar yana Kallonta da narkakkun idanunshi , hankalin kisna ya sake tashi  ita   ba maganarsa tafi daga mata hankali  ba  zuwan ahlinta tafi jin tsoro   dube  dube ta soma  tana addur  kar Allah ya kawo Aliyu ko  ya samir  guri, numfashi  ta sauke saboda  babu    alamunsu  hatta su anty zee bata ga kyallinsu a gurin  ba dan haka  ta  sanyawa jikinta natsuwa tare da gyara tsayuwar ta   ,bangaren Aliyu kuwa gabad'aya  ya manta da wata halitta kisna suka zo  tsabgar  gabansa kawai  yake yana gwadawa  areef takalma  , duk wanda ya daukar masa sai ya d'aukarwa aryan .."

Mutumin  ya lumshe idanunshi  yana jin yadda zuciyarsa ke tafasa akan jin abinda ta faɗa masa yanzu ,cikin murya mai cike da kasala ya cigaba da  fadin "gaskiya  gaskiya wanda ya aureki ya kassara min  rayuwa ,  ina ji ajikina koma waye ya aureki  baya sonki sai dai kasancewar mata nada   raunin  zuciya zaki iya son shi dan baku  san  mutanen da suka dace da rayuwarku ba ..."bata san sanda  dariyar maganarsa ta subuce mata ba  tayi  murumushi   tana   toshe bakinta  da hannuta,  aryan ya d'ago kanshi  ya kalleta ya sake maida idanunsa akan mutumin  dake tsaye ,"kin san wani abu"?ya tambayeta yana tsareta da idanunsa ,taki cewa komai saboda  qirjinta dake  bugawa da sauri "idan ace ni na aureki bazan Iya barin ki fita  ko'ina batare dani ba, irin kulawa da soyayyar da zan baki sai kin ce na rage  yayi yawa zan  lalla'ba....." saurin  katseshi tayi ta hanyar fadin "dan Allah ka wuce tare da mijina muke fa idan ya gamu  komai zai iya faru  ".ya zaro ido waje cike da mamaki "shine ya barki haka gaskiya hasashena ya tabbatar  gaskiya, wallahi baya sonki "hasashenka bai tabbata  gaskiya ba ni dai dan Allah ka rufa min asiri ka bar bibiyata hakan zai iya haifar min  da babban  matsala da mijina wanda bazan so faruwar haka ba ".

    "shikenan ya zanyi da rayuwata   zanyi  duk yadda kuke so sannan zanyi   addu'ar Allah  ya kawo  tsautsayin da mijinki  zai  sakar min ke  na aureki cikin kankanin lokaci dan bana son a dauki lokaci batare dana mallake ki ba  yayi maganar tare da mika mata badir din kudin kasar  "ga wannan ki sha ice cream ke da boy  taki  amsa tace  " bana  bukatar  haka daga gareka   , sannan ba Ameen ba  akan addur da kayi yanzu  saboda ina tsananin  son mijina duk runtsi bazan so rabuwa dashi ba  .."
Tabe  baki yayi kawai yana Kallonta sannan ya mika wa aryan hannu alamun yazo gareshi aryan   yayi saurin  makale kafad'a   ,"har yanzu  jikina yana  bani baki da aure sai dai  musamman  zan sa a binciko min komai naki   ina tabbatar miki nan da wani lokaci  zan san komai akanki   ya kamo hannun aryan da dabara ya daga shi sama yana masa wasa "ya sunanka boy "? Aryan daya jishi a sama yana yawo  daman abinda yake so kenan ya wangale  masa baki yana cewa  "aryan     ..." "Wooooowwww   nice name "  aryan   kace 

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login