Showing 123001 words to 126000 words out of 495987 words
Chapter 42 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
zai yi , idan ya mutu sai ni Allah bazan zauna ba, ganin haka yasa Aliyu sanyawa jikinsa kuzari haɗe da jarumta domin baya son rasa d'an'uwansa daya sauran masa a duniya , kuma baya son ya koma gurin mahaifinsu da sunan neman taimakinsa duk da bashi da tabbacin zai taimaka masa din , da kyar Hajiya kayi ta samu ta shawo kanshi yace ya hakura wanda a zahiri ne ya hakura amman a badini bai hakura ba ,dan ya rigada ya shiryawa barin garin ta kowani hali bayan sati daya da mutuwar nanyak aka nemi sadiq sama ko kasa aka rasa daga zuwa gona hankalin Hajiya kayi ya tashi tayita nemansa daga karshe ta samu labarin ya bar garin, ranar kam tayi kuka kamar ranta zai bar gangar jikinta har tayi data sanin haihuwar haroon arayuwarta ta rungume Aliyu ajikinta "Karka barni Aliyu ina tsananin sonka Karka gujeni "zaka rayu dani muddin rai ? "bazan gujeki ba yayi maganar muryarsa a dashe "zakayi hakurin zama dani acikin kauyen nan da babu wuta babu network babu jin dadin rayuwa ? "zanyi bazanje ko'ina ba zan kasance tare dake ta sake rushewa da kuka rayuwar yaron tamkar ba daga tsatson haroon ya fito ba kama ce kawai zai sa a dangantasu "na gode saboda kai muradi ne a zuciyata zan kula da kai da rayuwarka tana kuka yana goge mata hawaye , bayan kwana biyu ta tattara komai ta watsar ta maida hankalinta gurin kula da rayuwar Aliyu wanda a lokacin bai wuce shekara shida a duniya ba ,amman Allah yayi sa da kaifin baseera hankali natsuwa uwa uba ilimi ta kowani bangare ."
********
Cikin fushi da tashin hankali take Kallonsu daya bayan daya hankalinsu kwance suke bawa likita umarnin dubata ,kullum idan ta Kallesu haushinsu take ji acikin zuciyarta batasan lokacin da zasu qaunaci ya'yanta ba , ya'yan da bata da kamarsu a duk fadin duniyar nan , kullum da karyar da suke mata bayan umarni kawai zasu bata taje ta dauko ya'yanta tunda tasan inda suke , abinda ya faru ya rigada ya faru ya kamata ace komai ya wuce dan me bazasu hakura ba ,su barta ta rungumi yaranta , taja numfashi tana cizan lip's d'inta ta ƙara jingina bayanta da abun gado ranta na mata kuna, jira kawai take su sake cewa wani abu ta sauke musu abinda ke cikin ranta , likita ya soma ƙoƙarin daura mata drip har ya haɗa komai tana kallon wani gefe zuciyarta na zafi yana gama aikinsa ta fixge allura ta duro d'aga kan gadon tana huci kamar wata zautacciya , momy dake zaune a bakin gado ta mike jikinta na rawa ta kai hannu zata kamota ta zame "don't don't touch me momy ,mutuwar tsaye momy tayi tana dubanta a tsorace , dicter ta haɗe fuska tamau babu annuri acikinsa huci kawai take kafin ta fara magana cikin fushi da harshen yarensu "wallahi na tsaneku gabad'aya , kuma bana sonku acikin raina , ina mai tabbatar muku sai kunyi nadama mara amfani akan abinda kuka min ,kun nuna isarku kun rabani da ya'yana,kun gwamaci suyi rayuwar kauye babu wuta babu network babu komai na jin dadin rayuwa alhalin ina raye ,babu komai ta goge hawayen daya zubo mata " nasan inda na kaisu kuma zan koma na d'aukosu , daman nice bakwaso ba yarana ba, ku din yan'uwana ne amman kuka nuna bakwa son ya'yana wadan da nasha wahala reininsu , muddin baku lamunce min na daukosu ba, nayi muku alkwarin duk wani abu daya danganci jin dadin duniyarku sai na rabaku dashi koda kuwa ya'yan ku ne "
"kina hauka ne waye sa'anki anan "? " ko dan kinga ana lalla'baki ,bari kiji kije kiyi duk abinda zakiyi gidan nan ne baki isa kiyi rayuwa da wadan nan yaran ba sai dai ki koma ki karasa rayuwarki gurin wancan dillalin koken din ....."
Wani irin zummmmmm taji a gabad'aya ilahirin jikinta ,take zuciyarta ta soma bugawa da sauri sauri ta dinga Kallonsu daya bayan daya tana jin maganar eze wata iri cike da mamakin yadda suka san sa'ar uban ya'yanta "kin ɗauka bamu san aikinsa bane "?"ana ƙoƙarin rabaki da wahala kina tura kanki lokaci nake jira da kaina zan tama masa akamashi yaje ya karasa rayuwarsa a jail ,har yanzu babu wanda ya hanaki koma masa ga hanya nan ki ....
Tasssss tasssss eze yaji yatsun mahaifiyarsu akan fuskarsa wanda yasa take bakinsa ya mutu ya dafe daidai inda marin ya sauka "ka min shiru ,maganar dawo da yara ake ina ruwanmu da wani sana'ar ubansu , kar na sake jin ka faɗa mata kalmar da zata d'aga mata hankali ."
Wani mummunar ajiyar zuciya dicter ta sauke kana ta soma motsa bakinta alamun son yin magana amman ta kasa sai tari ta soma yi da karfi duk sukayi kanta suna kiran sunanta ta saidasu da hannuta tana dafe daidai saitin zuciyarta , suka tsaya tamkar an dasasu suna Kallonta a matukar tsorace , likita ya bukaci su matsa sai dai babu wanda yayi kokarin matsawa ,har sai da suka taimaka masa ya kwantar daita ahankali tarin ya dawo yana fita da numfashinta ,kafin kace me ta fara aman jini ,nan take sukayi asibiti daita ko cikkaken awa biyu basu yi ba likitoci suka fahimci zuciyarta ta tashi aiki, gaba-daya hankalin likitoci ya tashi dan sun san da wuya ta rayu sai dai suka kasa fadawa y'an'uwanta aka kwantar daita a wani kebantaccen daki aka daura mata ruwa ."
Bayan sati daya , tana kwance akan gadon marasa lafiya duk ta rame sai idanuwa ,ta motsa bakinta a hankali alamun magana , momy ta kawo kunnenta daidai bakinta dan bukatar jin abinda take buƙata "momy ki jingina bayana ina son na dan zauna tayi mgnr da kyar mommy ta tayar daita tasa mata pillow a bayanta suna kallon juna "sannu ya jikin "?
"Ai naji sauki anan asibin babana ya rasu ko momy "?Tayi tbmyr tana huci , mommy tace "Mai Kuma ya kawo maganar mutuwa yanzu"?
"Saboda nima mutuwa zanyi take momy ta rushe mata da kuka" dan Allah karki min haka, karki mutu ki barni, ta riko hannuta cikin nata tana kuka babu inda zaki tafi ki barni muna tare sai dai ni na tafi na barki ahankali dicter ta shiga shakuwa babu kaukautawa mommy ta mike da sauri ta kawo mata ruwa ta bata tana mata sannu ,kamar kar ta sha ruwa sai shakuwar tafi ta farko ,da sauri mommy ta nufi kofar fita dicter ta d'aga hannu tana kiranta alamun ta dawo , amman ina hankalinta baya jikinta burinta kawai ta isa ga likita tare da likita suka dawo dakin yana Kallonta yasan numfashinta ya dauke a gangar jikinta ta zama gawa , amman sai ya kwantar daita ya fara gwaje gwaje irin nasu na likitoci har na tsawon minti goma sannan ya bukaci mommy ta biyo bayansa ,ta biyosa tana waiwayen dicter dake kwance..."
Duk yadda momy taso jin wani abu daga bakin likita ya kasa yiwa mommy bayani komai illa ya kira number ema ya sheida masa halin da ake ciki ,a matukar haukace suka karaso asibinti , gabad'aya an rasa mai rarrashin wani sannan an rasa wanda zai fada wa mahaifiyarsu sai wata doctor ce ta sanar mata , tana gama dogon nasiha da faɗa mata abinda ya faru mommy ta zube kasa tana birgima tana kiran sunanta "shikenan komai ya kare min ema eze James kun sa na rasa tilon diyata ,ta mutu ta barni ,na tsaneku na tsaneku bazan taba yafe muku ba, ta mike a matukar haukace ta nufi dakin da dicter take kwance ta kwanta ajikinta tana wani irin kuka mai taba zuciya tana kiran sunanta "ki tashi karki tafi ki barni am bad mother ,mai yasa nayi miki haka "?
"Mai yasa ban tsaya miki ba tunda nice responsibilty dinki ,Mai yasa ya nemi shawarar yanuwanki a tun farko am bad mother for you tana gama fadar haka ta had'iye zuciya ta zube kasa shikenan bata sake motsi ba , take su ema suka yo kanta suna girgizata "mommy! mommy !! suna kiran sunanta da karfi plz mommy wake up don't do this to us we are really sorry mommy look at me eze ya fada yana haɗe fuskarshi da nata ,"mommy plz open your eyes ya fada yana sheshekan kuka ban da sautin kukansu baka jin komai acikin dakin likitoci suka yi cirko cirko suna Kallon irin haukan dasu ema suke yi tunda suke basu taba ganin mutuwa irin wannan ba ,a rana daya awa daya ne tsakaninsu , excuse me wani likita ya fada yana kokarin dagasu akan gawar mommy " plz live us like this "kuyi hakuri mahaifiyarku ta rigada ta mutu ,haɗa baki sukayi gurin kiran "mommy wake up .........kamar wasu kananan yara "shikenan mommy kin tafi ki barmu why mommy Mai yasa kika mana haka alhalin kinsan muna tsananin sonki ? "mommy you can't just live us like this Kafin kace me asibinti ya cika da yan'uwa da abokan arziki aka dauki gawarsu zuwa gida ,a tare aka kai su kabari kasancewar dicter na ciki ,da mommy ce kadai ta mutu sai an yi bikin mutuwarta sannan a binneta ,ga kabarin dicter gana mommy zagaye da fulawas kowa ya watse aka bar ema James da eze a gaban kabarin mommy da dicter suna kuka cikin bacci Aliyu ya farka da misalin karfe biyar na yamma bunkasa an binne mahaifiyarsa daman tun safe yake jin faduwar gaba sai dai rashin son magana yasa ya kasa fadawa Hajiya kayi yayi shiru yana jin tsananin faduwar gaba Hajiya kayi ta kalleshi cike da tausayawa "duk taga yayi wani irin ,duk sanda ta ga yayi irin wannan shirun to ya tuna da mahaifiyarsa ne "sannu muradina ka tashi ....."? dake sunan dake kiransa kenan ya gyada mata kai kawa "tashi kaje kayi sallah kaji ka kara sakawa ranka hakuri wata sai labari inshallahu zaka sake daura idanunka akan rashida ai kana son ganinta ? da sauri ya gyada mata kai hawaye na zubo masa . bayan gigin mutuwar ya sake su ema suka fara tunanin inda zasu nemo yaran dicter dan sai lokacin sukayi nadama, nadama mara amfani dan babu wata sheidar inda zasu samesu, dan har inda haroon yake a garin Abuja sunje sai dai an tabbatar musu da tuni ya bar garin ya koma ibadan da zama haka suka dawo benue jiki a sanyaye ......."
*******
sannu a hankali rayuwar Aliyu ta cigaba a hannu Hajiya kayi har ya cike shekara biyu agurinta komai nata muradi ne , komai ta samu tace na muradina ne ,duk abinda taci sai ta rage masa wanda zuwa wannan lokacin salaha tazo yafi sau uku duba mahaifiyarta tun zuwanta na farko taji Aliyu ya shiga ranta taso tafiya dashi amman yaki yarda saboda Allah yayi sa da gudun mutane gashi bashi da saurin sabo da mutane, kowa dari dari yake dashi sai dai bashi da tsoro kana kallonsa kasan namijin duniya ne ,kin amincewarsa yayiwa Hajiya kayi dadi dan itama bata son yin nesa dashi yana ɗebe mata kewa ta sanyawa zuciyarta mutuwace kawai zata rabata dashi ,a hankali tunani haroon yasa ciwo ya kama hajiya kayi tana son sake daura idanunta akanshi kafin ta koma ga Allah tun tana kirga shekarun datayi rabonta dashi har ta daina burinta dai ta gansa kullum cikin addu'a take masa akan Allah ya juyo mata da hankalinsa amman shiru ciwo kamar wasa sai gashi ya zama gaske sai kwantar sai an tayar hakan yasa Hajiya salaha ta tattaro ta dawo gurin mahaifiyarta ta ɗauke sai asibitin sir yahya dake birnin Kebbi gwajin farko likitoci suka tabbatar da ciwon zuciya ne nan aka daurata akan maganin ya'yanta na iyakar kokarinsu haka surukinta Alhaji realwan na turo kudi domin lafiyarta kullum hajiya kayi sai tacewa salaha " muradi ...."
"Karki damu zaki tashi ki cigaba da rikonsh watansu daya tace ga garinku Allah ya amshi rayuwar hajiya kayi a hannun tilon diyarta ,mutuwar data gigita Hajiya salaha tayi kuka kamar zata bita gbdy ta dawo abar tausayi , bayan an gama zaman makoki hajiya salaha ta nuna zata wuce da Aliyu idan zata koma Lagos amman y'an'uwanta suka hanata , garba yace" muddin ta kuskura ta dauki yaron babu shi babu ita har duniya ta nad'e ,mai zatai da jinin haroon mutumin da yayi sanadiyyar rasa iyayensu ina tabbatar miki yadda haroon yake haka ya'yansa zasu kasance ".
"kada ku manta jinin dake yawo ajinin haroon shi yake yawo ajinmu ,mutuwa kuma dole ce idan kwanan mutun ya kare ina da tabbacin kwanakin iyayenmu ne suka kare ba wai haroon ne ya kashesu ba ,dan haka babu abinda zai hanani d'aukarsa dan babu wanda zai rikeshi anan daya wuce mu ,"ki daukeshi amman babu saka hannuna aciki kuma duk abinda ya biyo baya babu ruwana wallahi". "naji zan sheidawa Alhaji muddin ya yarda zan daukeshi ta juya ta kalli Aliyu dake rakube ajikin kofar dakin yana saurarensu daya bayan daya tace "muradin Hajiya kayi zaka bini Lagos ?yayi shiru kawai yana Kallonta cike da tausayawa ta janyo hannunsa ta zaunar dashi saman cinyarta "zaka bini ko zaka zauna gurin Jamila ya ɗan gyada mata kansa alamun zai bita dan ya ɗan saba daita kasancewar tana zuwa gurin Hajiya kayi akai akai saɓanin fuskarsu Garba da tun zuwansa sau daya kawai suka kawo ziyara "yauwa muradi ta furta tana shafa kanshi," zaka zauna gurin jamila idan an kwana biyu zan sa azo a tafi da kai kaji yarona ya sake gyada mata kai watanta daya ta bar garin da zumar zata sa a zo a dauki Aliyu idan mijinta ya yarda .."
Koda Hajiya salaha ta tari mijinta da batun dauko Aliyu kin yarda yayi abun yayi matukar bata mamaki ,abinda batasani ba y'an'uwanta ne suka zuga shi kar yarda a daukosa ,wannan rashin amincewarwa ya tsaya mata arai har ta dinga masa wani irin kallo saboda a lokacin tana rike da zahra mufeda yaran d'an'uwansa da ya rasu ya bari ,bata taɓa nuna gazawarta akan yaran ba yadda take kulawa da yaranta haka take kulawa da zahra da mufids amman shi dan d'an'uwana kwaya daya zai hanata daukowa tayi kukanta ta hakura ,sai dai ta dauki alwashin zata inganta rayuwar yaron cikin wannan lokacin ta samu labarin dawowar sadiq abun yayi mata dadi sosai tace shima ya zauna gurin jamila kafin tasan abun yi ,kullum sai tayiwa mijinta naci da rokon ya amince mata ta dauko Aliyu har tsawon shekara biyu wanda a lokaci kauyen ilo ya samu network din glo , kuma sai a wannan lokacin ya amince mata yace a tawo har da sadiq aiko ranar yaga abun mamaki dan har da sadakar wake da shinkafa tayi tsabar murna ya dinga mamaki irin farinciki da take da irin soyayyar da takewa yaran, hatta ya'yanta sunga sauyi atare daita, batare da bata lokaci ba ta kira Jamila tace ta biyo mota ta kawo sadiq da Aliyu tunda ita tasan hanya dan kusan a Lagos tayi rabin rayuwarta da mijinta kafin ya rasu washegari gari alhaji realwan ya shirya zuwa kano bikin wani yan'uwansa ,Hajiya salaha ta shirya masa kaya har gaban motarsa ta rakosa sai data ga ya shiga sukayi sallama direba yaja motar zuwa airport sannan ta komai ciki tana masa addu'ar ta kira number Jamila tace su shirya zata tura musu da kudin mota ranar monday tazo da sadiq da muradi . "Suna gama waya ta sanarwa sadiq take yace mata bai zuwa ko'ina shi ta bashi kudin motarsa zai koma abuja ko zai samu labarin inda mahaifinsa take ita kuma tace sai dai ya zauna amman bazata bashi sisi ba yace "to bai zuwa kuma bazai zauna a ilo ba ta kira Hajiya salaha ta sheida mata tace a bashi waya tayi masa magana yaci yaji amman tun ranar Lahadi aka nemishi aka rasa .."
********
Zaune mutane suke a acikin mota kirar bus Mai cin mutun goma shabiyar Jamila ce zaune a gidan baya da Aliyu da bai wuce shekara goma da haihuwa ba ,tayi shiru tana tare da zabga uban tagumi a tun sanda suka taso daga kauyen bagudo dan suka samu mota mai zuwa lagos direct tun taso warsu babu abinda take sai tunani a cikin zuciyarta gabad'aya tunaninta ya yafi ne akan sadiq ɗaya ce bazai biyosu ba shi neman ubansa zashi alokaci da bai wuce shekara 11 da wani abu ba wai bata son zuwan nasa bane aa bakunta a ko'ina yana da matukar wahala ,tafiya mai tsawo motarsu tayi Amman har lokacin basu ci rabin tafiyar ba a hankali ta janyo Aliyu ta kwantar ajikinta tana shafa laulausan sumar kanshi mai kama data ainihi zarma , tana jin Aliyu aranta tamkar dan data haifa dan akwai shakuwa mai karfi a tsakaninsu ,ko kwana uku kayi da Aliyu zai shiga ranka bare shekaru masu yawa ,a hankali bacci ya dinga fixgarta dan haka ta lumshe idanunta domin ta ɗan runtsa tunda zuwa birnin iko ba yanzu ba har sai garin Allah ya waye ......"
direba yayi saurin taka burki , sakamakon katon gungume daya tarar akan hanya an gicciye shi gaba-daya mutanen dake cikin motar suka fara salati da sallami tuni masu bacci suka wastake ciki kuwa har Jamila da Aliyu ta kwakwame Aliyu ajikinta tana furta "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun cikin rawar jiki tsayawar motar ke da wuya sai kuwa suka ga wasu mutane sun fito daga cikin
dajin su goma sun kewaye motar .... "
Mmn Sudais
[7/19, 5:32 PM] +234 803 631 5951: 💗💗💗💗💗💗
CUTAR DA KAI
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Page 20
~TRUE LIFE STORY~
*PAID BOOK*
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
"Wannan littafin na kudi ne ,mai bukata karanta shi zai tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number alert +234 803 238 4602 domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only