Showing 84001 words to 87000 words out of 495987 words
Chapter 29 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
wanda ba'a son muslimi yana yin haka ta kamo hannu kisna ta saka cikin na Aliyu ta dunkule guri daya " ka yafe mata wannan alfarmata ce na nema agurinka nasan ko numfashinka nace ka bani zaka mallaka min bare kalmar baki ,Shiru yayi har kusan second biyar "kayi shiru muradi kace ka yafe mata ? Da kyar ya sake buɗe baki yace "na yafe amman darajanki ne mumy wani sanyayiyyen numfashi Kisna ta sauke tana mai godiya ga Allah da ya furta ya yafe mata mumy tace "nasani darajana taci kuma na gode ko alahira wani nacin arzikin wani Allah yasa muci arzikin Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama "ameen suka hada baki..."Sai abu na gaba Kisna zan baki wata biyar ki dawo da Aliyu daidai ,kaima Aliyu zan baka wata biyar ka dawo daidai da matarka idan ba haka ba zan ɗauki mummunar mataki akanku wanda a karshe bazai muku dadi ba, tana gama fadar haka ta mike da kyar ta soma kokarin barin dakin Aliyu ya mike zai taimaka mata tace "yi zamanka muradi na gode zan iya takawa da kaina ya koma ya zauna yana furzar da numfashi .."
Mommy na tashi daga mazauninta Kisna ta mike cikin sanyi jiki ta biyo bayanta ,mumy dake kokarin zama ta dubeta a tsanake tace "me kuma kika zo yi ? " Maza ki koma gurin mijinki ki soma aiwatar da aikinki Allah ya baki nasara akanshi muryata a shagwabe tace "mumy wannan dan naki fa akwai wuyar sha'ani kanshi kamar kwakwa yake wallahi "ungo nan haka zaki daure , tun farko da bakiyi abinda kikayi masa ba kema kinsan yadda kike so zakiyi a gidansa ,hakuri zaki kara akan wanda kike yi , ki sanyawa ranki ibada kike yi kin san kuma duk abinda akace ibada ne dole sai an d'aure tare da sanyawa zuciya hakuri inshallahu ina ji ajikina zakiyi nasara akansa bazai sake wining zuciyarki ba "shikenan mumy adduarki ta Kara min karfin gwiwa daga sarewar dana yi da lamarinsa dan wallahi har na cire tsammani a kanshi "ba'a cire tsammani da rahmar Allah mamana ,kuma inshallahu sai kinyi alfahari da mijinki wata rana mumy ta dan dauki lokaci tana bata shawarwari daga karshe sukayi sallama ta koma dakin yana nan zaune a inda ta barshi yayi tagumi
ta matsoshi sosai kamar zata shige jikinsa sauran kaɗan ta kwanto jikinsa tace " maganar mumy gaskiya ne bazamu iya rabuwa da juna ba sai dai wallahi na gaji da irin rayuwar da muke ka saki ranka mu zauna lafiya , ni dai nasan a halin yanzu babu abinda nake son kasancewa dashi kamarka bazan iya rayuwa babu kai ba , ina sonka aliyu kaima nasan kana sona "? tayi maganar tana murza tafin hannunsa dake cikin nata ..."No i can't ya fada atakaice yana furzar da iska mai zafi tare da jan dogon tsaki , shiru tayi jikinta na ɗaukar rawa "you mean you don't love me "? "yes I do ya sake bata amsa a takaice ,ta sake matsoshi tare da sanya kwayar idanunta cikin nashi, d'ayan hannunsa ta kamo ta mikar dashi tsaye "come with me ta nufi jikin bango dakin dashi bai mata musu ba yayi shiru yana biye daita kamar wani karamin yaro suna karasawa ta tsaida shi tana fuskartashi tare da kai hannuwanta duka kan wuyansa ta zagaye tana jifansa da wani irin kallo mai kashe gabobin jiki "meye haka kuma "?yayi magana yana kai hannunsa zai cire hannuwanta dake zagaye da wuyansa "tsaya mana ranka shi dade ka ga wani abu , ta cire hannuwanta dake zagaye da wuyansa ta zuge zip din gaban rigarta take dukiyar fulaninta dake cike bammm sunyi wani luhu luhu dasu ga kyau ga haske ga taushi suka bayyana a gabansa "wowwww is beautiful yaushe rabon na gansu ya faɗa acikin ranshi amman a zahiri tsaki yaja yana kawar da fuskarshi gefe kamar yaga mugun abu ,ta kai hannunta ta dawo da fuskarsa gareta ya sake dauke idanunshi akansu "duk fa wannan kayan marmari is for you Aliyu muradi ".... "for me"? ya furta yana watsa mata harara "Yes of course is for you don't you like it ta sake turo masa su daidai bakinsa kasancewarta doguwa sosai kaɗan ya rage bata kamoshi ba yayi saurin runtse idaunshi qirjinshi na wani irin bugawa da karfin gaske "stop all this nonsense Kisna it not look beautiful ",kinsan wani abu "?ta girgiza masa kai tana tura hannunta cikin vest d'insa har tayi nasarar kife yatsunta a qirjinsa ya bude baki da niyyar zai yi magana ta muzra kan nipple's d'insa duka tana wani irin narke masa ajiki ... ...tsarkewa yayi ya soma tari kamar wanda yaci wani abu mai yaji take ta rude tana masa sannu "na kawo maka ruwa "?Kai kawai ya girgiza mata alamun a'a ya zare hannunta daga jikinsa ya nufi gaban mirrow yana magana yana kwance agogonsa sai lokacin ya samu damar fadar abinda yake son fad'a mata " duk wannan abinda kike yi basa burgeni saboda bana jin komai ajikina ji nake kamar namiji ne a kusa dani ,wallahi na gaji dake bazan dai iya fitowa na fad'awa mommy bane dan ita kadai zan iya gama rayuwata dake ba dan ina sonki ba,idan son samuna ne ma wallahi nayi nisa da rayuwarki zai fiyye min kwanciyar hankali.."
"look I understand what's in your heart ,ba Sai ka faɗa min ba saboda idan da sabo na saba da wannan kiyayyar ko zan iya baka tukuici akan wannan kiyayyar "?yayi shiru yana Kallonta ta cikin mirrow zuciyarsa na tsalle kallon wawiya yake mata ita kuma tana masa kallon mara wayo "bana bukata kuma karki dameni da shirmeki na banza on-expecting yaji ta sumbaci kumatunsa ta juya tana wata irin shegiyar tafiya tana kad'a masa jiki wanda ya zame mata jiki a tsorace ya juyo yana kallon bayanta "kina hauka ne kike irin wannan tafiyar "? "Haukan sonka ba ta bashi amsa tare da juyowa suna fuskantar juna "me kuma ya samu tafiya ta ? tayi magana tana matsowa a hankali ta karaso gabansa ta tsaya kirjinta na kadawa shiru yayi tare da tsura mata ido kamar zai cinyeta ganin taki ɗauke idanunta akanshi ya cire vest dinsa yabi gefenta zai wuce Kawai yaji ta rungumeshi a jikinta , hannuwanta ya sauka a daidai kan nipple's d'insa wani irin shock yaji a ilahirin jikinsa "dan Allah ka bani wata biyar kamar yadda mommy ta fada ina tabbatar maka kafin lokacin soyayyata zatayi tasiri a cikin zuciyarka am very sure zaka soni kafin lokacin "no ya furta a zuciye "ya Aliyu Ni dai ka bani dama dan Allah nayi maka alkawarin muddin baka soni ba zuwa lokacin zan daina sonka gaba-daya zan rufe babin wani Aliyu a rayuwata zaka rabu dani batare da sanin kowa ba, zanyi nesa da rayuwarka a hankali take masa magana cikin rada tana shafa qirjinshi tana manna masa kiss a wuyansa, juyo wa yayi daita a hankali aiko ta fada cikin faffad'an qirjinsa mai kwance da kashi sai kamshi yake zubawa " wayyo my world best wallahi bazan iya rayuwa babu kai ba sonka yayi mugun kamani ta karasa mgnr tana mirza kan nipples d'insa yayi saurin runtse idanunshi shi kadai yasan yadda yake ji a lokacin ,a hankali ta cigaba da murza nipples dinsa tana sauke ajiyar zuciya sannan tana lumshe masa idanu, ta zaro harshenta daga kwance da take ajikinsa tana lasar tsakiyar qirjinsa yayinda hannunta ke kan nipples dinsa tana zagayewa tana fitar da numfashi tana jin wani mugun feeling na taso mata a gaba-daya ilahirin jikinta kamar yadda shima yake ji ,gaba-daya gobobin jikinsa sun soma macewa saboda amsar sakonninta, jin yanayinsa yana neman sauyawa yayi sauri cire hannuta a kan nipples dinsa ya bude idanunshi sosai yana fidda numfashi yana kallonta yana jiran ta bar jikinsa ,sai dai bata d'ago ta kalleshi ba ganin idan ya barta ta cigaba komai zai iya faruwa dashi daga karshe tayi galaba akanshi tun ba'a je ko'ina ba ya fixegeta da karfi yana ƙoƙarin makata akan kujera ta janyosa ya fado jikinta tare da rungumeta .. "ashhhhh ta saki yar qara saboda q'irjinsa daya sauka akan dukiyar fulaninta ya kalleta da sexy eye's d'insa , muryarta cike da shagwa'ba wanda ke kara burge mutane kuma take rikita duk wanda ya saurara tace "my world best ka bani dama dan Allah tsaki yaja ya mike tsaye yana fidda numfashi mai zafi sannan ya nuna ta da yatsan hannunsa alamun gargadi " na yafe miki ba lallai sai na soki ba ki cigaba da tsayawa a matsayin ki na uwar Aryan da areef yana gama fadar haka ya shiga bathroom tayi dariyar jin dadi "yafa ji dadi haduwar da jikinmu yayi amman dan wulakaci ya wani maze Ina nan har ka fito ......."
tana zaune a inda ya barta yayi wanka ya fito yana goge jikinsa da white towel ta mike zata taimaka masa ya dakatar daita "thank you.."
"Please! please now !! Ka bari na taimaka maka gabad'aya ya haɗe rai fuskarsa babu walwala bare annuri ,sosai ta dinga rokonsa ganin nacinta yayi yawa ya barta sai dai babu abinda ya furta mata" you're my life I love you muradi I can't live without you duk duniya yanzu kai ne kawai abinda nakewa tsananin so dan Allah ka bani wata biyar din nan muddin ban shawo kanka ba na yarda ka sawwake min ko a boye ne naje nayi rayuwata a wani guri bazan sake dawowa cikinku ba zan barku kuyi rayuwarku i promise ajiyar zuciya ya sauke a hankali yana jin wani sabon yanayi na qara shigarsa muryarsa can qasa qasa yace "na baki ya fada a takaice ....."
Wani irin sanyin dadi ne ya ziyarceta taji kamar tayi tsalle ta rungumeshi ajikinta amman tasan halinsa yanzu zai iya dangantata da kalmar hauka ko janye amincewarsa a hankali ta ji wani sabuwar qaunarsa na qara shigarta muryata a sanyaye tace "thank you my world best kuma inshallahu zan yi nasara" tsaki yaja jikinsa na qara mutuwa saboda har cikin jinin jikinsa yaji sautin muryarta data sauka a cikin kunnenshi shiyasa gabad'aya ilahirin jikinsa ya mutu murus ..."
Ya kalleta ta cikin mirrow yaga yadda take murna a fili ya girgiza kanshi yana tsuke karamin bakinsa "bazaki taɓa samun wannan damar ba shiyasa na baki dan bazaki taba zama acikin rayuwata ba bare zuciyarta "yayi maganar a kasan zuciyarsa itama zance zuci take tana kallonsa tana murmushi tare da watsa yatsun hannunta cikin tsananin farinciki "zan canza ka ya Aliyu na yiwa kaina alkwarin zaka soni da dukkanin rayuwarka "muje kaci abinci shiru yayi yaki cewa komai har tsawon minti goma ta sake yin magana ciki raunanniyar muryarta kamar zatayi kuka "dan Allah muje kaci abinci da alamun kana jin yunwa kalli yadda cikinka ya lefe ban san mai yasa kake kin cin abinci ba ko nayi maka tuwon shikafa da miyar wake ? ta karashe maganar a hankali , da kwantar da kai da rarrashi ta samu ya fito tana biye dashi abaya suka sauko parlou'n kasa lokacin babu kowa sai aunty zee da Samir zaune akan kujera suna kallo tayi saurin karasowa taja masa kujera "na zuba maka abincin da mommy ta girka ko na shirya maka wani?"no .... Ya fada tare da ɗaukar jug dake cike da ruwa ya kai bakinsa ta dauki plet ta zuba masa farar shinkafa da miya ta ajiye a gabansa tana jin kamar ta bashi a baki kusan minti biyar yana kallon abincin sannan ya fara ci hankalinsa a kwance saboda jin abincin mommy ne ,ta tsaya tana kallon shi fuskarta kwance da murmushi ta lumshe idanunta saboda tsananin dadi shi kuwa tunda ya soma cin abinci ko kallon inda take bai yi ba ,aunty zee ta zuba mata ido tana Kallon Kisna sai murmushi take tana kallon Aliyu ko kifta idanunta bata yi akan shi "ya Aliyu ya sauko daga dokin fushinsa ne yasa Kisna take murna murmushi haka "? abinda ya baka tsoro wata shi zai baka tausayi shiyasa Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama yace "idan zaka so mutun ka so shi kadan haka zalika idan zaka ki mutun kaki shi kadan yau dai ga Aliyu ya tafi da rabin rayuwar kisna ya bar saura ,waigowa Kisna tayi aiko idanunsu ya haɗe dana aunty zee take ta sakar mata harara bata damu da hararar da aunty zee tayi mata ba , ta kai hannu ta tsiyaya masa ruwa garin rawan jiki ruwan ya zube a ƙafarsa daya tsaki yaja tayi saurin cewa "sorry ta warware tissu ta tsuguna ta goge masa ta bar gurin tun kafin tayi wani sabon laifi ta dawo inda aunty zee take ta kwanta ta daura kanta akan cinyar aunty zee tana jin dadi "ina miki fatan samu soyayyar wanda kike so dan ki damgwama cikin farinciki tayi maganar tana shafa sumar kanta kallon fuskar aunty zee tayi tana sake fadada fuskarta "Ameen auntyna Allah ya barki da ya samir "na gode sister ina miki fatan samun nasara ki samu soyayyarsa nan kusa sannan ku so juna har abada d'agowa tayi ta zauna idanunta cike da ruwan hawaye "mumy ta Bamu wata biyar mu daidaita kanmu ko kuma ta dauki mummunar mataki akanmu, ni kuma na nemi alfarma wata biyar agurinsa aunty zee zan yi ko'k'arin naga na shawo kansa duk da nasan da wuya hakan ta kasance ,wallahi ina tunanin halin da zan shiga idan na kasa shawo kanshi aunty "da Ikon Allah Zaki yi nasara akanshi mutun ne fa shi kuma mai jini ajiki, kuma bai fi karfin Allah ba ki tsaida zuciyarki kisa a ranki zaki shawo kansa hawaye ya soma gangaro mata a lokacin daya mike rike da wayarsa dake qara ya nufi haraban gidan ......."
Da sauri aunty zee ta rungumeta itama ta rungumeta aunty zee gabad'aya jikinta yayi sanyi a hankali suka cigaba da tautaunawa zuciyar kowannensu cike da tunani har kusan 11 sannan suka yi sallama da juna ta nufi dakin mommy wacce tuni tayi bacci da jikokinta ta zauna a bakin gadon ta janyo man zafin dake gefen kanta wanda duk daren duniya dashi take kwana ta lakato ta mulka a kafarta tana mammatsa mata kafa zuwa kaurin gwiwarta mommy ta motsa a hankali tare da ɗan bude idanunta kadan "bakiyi bacci kisna .."? "Yanzu nake shirin yi nace nazo muyi sallama sai gashi kinyi bacci numfashi ta sauke tana lumshe ido ta ɗan dade tana mammatsawa mommy jiki kafin daga baya mommy tace "mamana tashi kije ki kwanta kin bar mijinki shi kadai "to mommy har ta mike ta dawo daidai fuskar mumy ta tsugunna "mumy ki yafe min " me kuma kika yi" bakiyi min komai ba mamana "Ni dai kice kin yafe min "
"Na yafe miki mamana Allah yayi albarka " ameen sai da safe ta karasa inda yaranta ke kwance ta shafa sumar kansu tare da shafa musu addu'a , ta manna musu kiss a goshi sannan ta nufi dakin baccin su har ta karasa shiga d'akin tunanin Aliyu take da irin badaudaden halinsa mai wuyar sha'ani tana tsaka da tunani idanunta ya sauka akan calander a manne a bango dakin jiki a sanyaye ta karasa jikin calander ta tsaya tana kallo a karshen shekarar ake ta dubu biyu da sha takwas "kenan a may yarjejeniyarsu da Aliyu zai cika "ya Allah ka taimakeni na shawo kansa kafin lokacin ta dauki bironsa dake ajiye akan table tayi mark din aikinta na farko data yi na nasarar janyo hankalinsa ya yarda da tsarin da mommy ta gindaya musu sannan tayi nasarar da yaci abinci cikin sauki batare da tashin hankali ba taja numfashi ta sauke sannan ta shiga wanka tayi ta fito ta goge jikinta ta dauko daya daga cikin kayan da aunty zeey ta kawo mata ta saka rigar bacci iya cinyarta mai bud'ad'd'en gaba sai wata yar igiya da'aka saka domin daurewa ta tufke sumar kanta a tsakiyar kanta dan taji dadin bacci ta fesa turare ta saki murmushin jin dadi ta haye saman lafiyayyen gadon mijinta ta kwanta ta rungume pillow a qirjinsa tana jin kamar shi ta rungume tana kwance taji shigowarsa tayi saurin runtse idanunta kamar mai bacci ,wayarsa yasa a handsfree muryar nawal taji ta karade d'akin take gabanta ya shiga dukan uku uku ta ɗan bude idanunta kadan taga ya dauko computer dinsa ya ajiye akan table ya jonata a caji still tana jin sautin muryarta har ya zauna "do you miss me nur? murumushi kisns taga yayi sannan yace "Yes dear I really miss you ya fada fuskarsa na wanzuwa da wani sabon murmushi data kasa fahimtar na menene a hankali yake operating din system dinsa yana saurarenta can ya ciza lip's d'insa muryarsa a kasalance yace"okay tell me how much you love me ? ya fadi haka ne saboda lura da yayi idanun kisna biyu akanshi "I can't discribe the way I love you amman kasa a ranka zan soka har karshen rayuwata kai ne kadai zaka mallaki zuciyata sannan ka zauna a cikinta har sanda za'a zare numfashina ......" ya rasa me mata suke gani ajikinsa suke leke masa har su maida shi duniyarsu da numfashinsu shiru dukkaninsu sukai na tsawon lokaci can muryarta ta sake bayyana "yasu aryan da areef sunyi bacci ko "? Yace "uhmmm yana cigaba da danne danne "ya tafiyar mommy tana nan jibi din "? ya sake cewa uhmmm ",okay zanzo airport inshallahu muyi sallama kuma gobe zan turo direbana "okay ya fada a takaice dan ya soma gajiya .
a hankali kisna ta sauko daga sama gado ta bude wardrobe ta dauko bargo guda biyu ja da fari ta masa ja akan gado daga gefe guda tare da pillow , zata koma dayan bangaren katifa taji yayi gyaran murya ta tsaya haɗe da juyowa ta zuba masa kyawawan idanunta "ki dawo ki kwanta a kasa "inna lillahi ta furta a kasan zuciyarta yayinda a zahiri