Showing 333001 words to 336000 words out of 495987 words
Chapter 112 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
tsaye wata budurwa ta karasa kusa dashi ta amshi jakar hannunsa suka jera tare wajen shiga jirgi wani abu taji ya caki zuciyarta nan take damuwarta ta fito fili haka nan taji kamar tayi kuka ",kada ki damu kamar yau ne zasu dawo inshallah maganar aunty ummi taso ta bata dariya daga ɓacin ran data tsinci kanta sai wani rarrashinta su aunty mufeeda suke kamar tace musu ta damu da tafiyarsa sai bayan da jirginsu ya tashi suka wuce gida suna sauka ita ya fara kira yace sun sauka lfy ",kina ina yanzu "?ya tambayeta "ina gidan zee ban koma gida ba ina nan yace ",oky take care of yourself tace ",uhm " kawai ya katse kiran duk sanda zee taga tayi shiru sai ta dauka ko tunanin muradi take sai tayita rarashinta tana cewa "kamar yau ne zasu dawo wata biyu zuwa uku babu yawa ita kuma sam ba tafiyar tashi ce ta dameta ba ,tafiyarsa ma hutu ta samu da rabar jikinta da yake yana mata kallon sha'awa ...."
Muna saida ingantattun maganin mata masu kyau da nagarta wanda ko da kudinka sai da rabonka tsimi , zumar Mata, gunba, gari insertion,kaza,zakara ,
jigida dadai sauransu.
1.Tsumi Yana saukarwa mace niima Kuma bazataji wuyar jimai ba.
2. Zuma Tana taimakawa wurin Jin sha'awa Kuma itama Tana taimakawa wurin jindadin jima'i.
3.insertion( Dan matsi) daban dabanne akwai Wanda ke matse mace kuma yake saukar da ruwan ni'ima sannan akwai na mallaka , idan ana bukata a tuntubi wannan number
234 815 945 0159..
Mmm Sudais[7/19, 5:32 PM] +234 803 631 5951: 💗💗💗💗💗💗
CUTAR DA KAI
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Page 49
~TRUE LIFE STORY~
*PAID BOOK*
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
"Wannan littafin na kudi ne ,mai bukata karanta shi zai tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number alert +234 803 238 4602 domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne . "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi za'a iya tuntu'bar Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos lace da kamfala ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da chiganvy, voyal lace duk akan farashi mai sauki ,ga mai bukatar siyan ɗaya ko sari yayi magana ta wannan number 08059623096.
... Suna zaune tare da zee a part dinta Kiran muradi ya shigo wayarta taja tsaki zee da tafi kusa da wayar ta miko mata ,Kisna na amsa wayar ta danna reject "haba Kisna wai ke har yanzu bazaki dawo hankinki ba rayuwar ma guda nawa take ?"wallahi bamu da lokaci fa saboda mutuwa mijin aurenki ko bai ci darajan komai ba yaci darajan aurensa dake kanki tunda yanzu aljannarki na karkashin kafafunsa gaskiya ki canza . tunda zee ta fara magana Kisna batace mata "uhm ba bare uhmmmm sai aikin furzar da iska take , itama aunty zee tayi shiru tana dubanta tare da mata addu'ar shiriya , can bayan kamar minti biyar wani kiran ya sake shigowa wannan karon a fili taja tsaki tare da furta" matsala" sannan ta dauka ta manna wayar a kunnenta tayi shiru taki cewa komai har sanda muryarsa ta doki dodon kunneta "ya kike fatan kina cikin koshin lafiya ? " Ta amsa da " lafiya "atakaice...
" kina ne ina ne part dinki ko na zee ? "ina part din aunty zee "me kike yi yanzu ? "Ina hutawa" da kyau amman ya kamata ki maida hankali ki dinga koyon wasu abubuwa agurinta a dan hassale tace " kamar me kenan "kamar girki da sauransu" "dan Allah malam ka rabani da wahala dan babu wani girki da zan koya wanda na iya ma ya isheni yace "a'a kiyi ƙoƙarin koya dan Allah a gatsine ta amsa masa da "to " kawai saboda ta gaji da jin muryarsa "ammm kina jina ..."dan Allah dan Annabi na gaji haba " ta katse kiran tana ajiye wayar a gefenta kamar jira zee take ta ajiye wayar cikin fushi tace "kai Kisna haka ake magana da miji a fusace ? ko Ni kin taba ganin na amsawa yayanki waya haka kamar ba mace ba ko a gabansa ko a bayansa ba haka ake amsa waya ba dan Allah ki koyi yadda ake magana da miji, duba kiga ko darajan suna bai samu ba a wayar ki sai surar numbersa wallahi idan kika yi sakaci na waje suka samu kanki zaki cuta zee ta karashe maganar tana ɗaukar wayar ta rubuta mata suna daga number zuwa my world best .."
Da daddare bayan ta kwanta wayarta dake kusa da pillow tayi ringing ta kai hannu ta dauka my world best ya bayyana a screen din wayar ta dauka tana yatsine yatsine ala dole an takura mata "hello " daga can bangarensa yace "ko har kin fara bacci ne naji muryarki wani iri ?"
"Uhm "kawai tace masa "ko dai kema kin fara kewata ne kamar yadda nake kewarki ? tace " oh daman ni ce maka akayi zanyi kewarka ? ni wallahi dadi naji da baka nan ,ni bansan ka zame min alakakai ba ma sai da baka nan yadda lokaci kadan na manta da wata damuwa gaba-daya na ma canza har wata kiba nayi "..
Idanu muradi ya runtse yaji maganar data gaya masa har cikin zuciyarsa Murmushin nan nashi mai matukar bayyana ainihin kyansa yayi ya danne abinda yaji tare da cewa "Hajiya kayi kenan ko zaki iya gaya min irin takurawar da nayi miki har kike murna da tafiyata ? kin ga kuwa ni ba karamin kewarki nayi ba musamman yadda kike kukan bakya sona ko zaki iya min kukan naji yanzu ? Tayi masa banza tana rike da wayar qirjinta na wani irin bugawa da matsanancin karfi "ko kuma kin daina kukan kina yanzu ?
" Ai wannan kukan na har abada ne bazai gamu ba kullum yinsa nake har sai ranar daka dawo ka bani takardata na kara gaba na huta da jaraba " dariya ta kubce masa har cikin kunnenta ya ɗauki Cup din coffe dake ajiye a bedside dinsa ya kurba ya cigaba da janta da magana , ita kuma bata sake ce masa komai ba tunda ta gane yau salon wayar nashi ya zamo har da rainin hankali yace "kinyi shiru kina jina bakice komai ba alhalin ni kuma na kira dan muyi hira ne "a fusace tace "hira fa kace kamar an gaya maka ni radio ce ko ance maka aikin jarida na karanta ne ?"
ganin yadda ta hayayyako masa yayi saurin cewa "Shikenan sai da safe Allah ya tashemu lfy tun bai kashe wayar ba ta cire a kunneta tare da jifa dashi taja tsaki tana furta "wallahi ka dawo ka sallameni na kara gaba dan nagaji da zaman banza kullum sai juya ni kake kana neman sakawa zuciyata hakuri zama da kai wallahi hakurina ya kare ka dawo ayi duk burouban da za'a yi ka sawwake min wannan jarababben auren naka ... ."
********
kwana sittin kenan wanda yayi daidai da tafiyarsu muradi ciwon ciki , ciwon baya ciwon qirji suka sarkafe Kisna komai taci sai ta amayar bata samun natsuwa har sai idan bacci ya dauketa , batare da wani bata lokaci ba zee ta fahimci ciki gareta ,zee ta kalleta tana murmushin jin dadi batare da tace mata komai ba "aunty zee ina zan samu tuwo miyar kuka ? " Ina zaki samu kuma bayan gani zaune aikin me nake yi ?" bari naje nayi miki na dawo ai duk abinda kike so ki fada min zan miki kanwar mijin matar yayana sukasa dariya cikin kankanin lokaci zee tayi mata tuwo semoviter da miyar kuka wanda yaji kashi mai nama sai dai tana gama ci tuwon tayi hanyar bandaki da gudu ta tsugunna ta shiga kwara amai aunty zee ta karaso da sauri ta tsaya a bakin kofa tana kallonta tana mata sannu bayan ta gama ta jingina bayanta bangon bayin tana nishi sama sama aunty zee ta k'arasa shigowa cikin bayi , ta wanke mata baki da fuska ta taimaka mata tayi wanka ta kamota suka dawo daki ta canza mata wasu kaya sannan ta kwantar daita tana rawar sanyi ta dauko bargo ta lullubeta sannan ta kwashi. kayan data bata ta fita ta kira wayar aunty ummi ta fada mata tace idan zata zo tazo da doctor Amman kada ta bari Kisna tasan tana dauke da ciki " cikin kankanin lokaci aunty ummi suka karaso tare da wata nus dake unguwarsu ta bugaci fitsarin Kisna tayi mata gwaji ta tabbatar da ciki ne na wata biyu da kwanaki nan ta bukaci a bata kudi zata suyo drip domin kara mata dan jikinta yayi week sosai aunty ummi ta bayar ta fita ,nus tana fita suma suka dawo parlour Suna hira har sanda nus ta dawo suka koma dakin tare ta daura mata drip wanda ta zuba alluran karawa jiki karfi anan suka ci abinci dare sai gurin takwas sukayi musu sallama nus da aunty ummi suka wuce gida babu laifi washegari Kisna ta dan samu sauki dan har hira sukayi da aunty ummi da zee daga karshe ta kama hamma tare da lumshe ido hakan ne yasa aunty ummi ta mike ta musu sallama "sai gobe idan Allah ya kaimu ke kuma kiyi bacci ki huta dan da alamun bacci kike ji "Kisna tace "to " still dai bayan fitar aunty ummi bata runtsa ba suka ci-gaba da hira da aunty zee a hankali a hankali bacci yayi awon gaba daita ."
Bayan sati Uku kisna
tana sallar isha'i a zaune saboda jikinta babu kwari wayanta ya kama ringing har ta idar ba'a kara kira ba bayan ta shafa addu'a bata duba ba dan tasan bai wuce mutumin data fi tsana ne akan komai dake cikin duniyar ba , ta mike tana nade abun sallah wayar ta kara daukar sauti ta dauka "hello" bayan ya amsa yake ce mata "ina kika shiga ne ina ta kiranki ko bakya kusa da wayar ne ?ta rasa abinda zata ce masa kawai ta amsa masa da "eh". Ya sauke naunauyen ajiyar zuciya sannan yace "daman zan gaya miki ne mun kammala abinda ya kai mu amerca har ma na samu lambar kwarewa tace ",?uhm yayi ni dai yaushe zaka dawo ka sawwake min aurenka dake kaina na kara gaba ?shiru yayi zuciyarsa na dokawa da matsanancin karfi sai dai yayi karfin hali ya sanyawa jikinsa jarumta yace " karki damu ai ni nace miki zan sakeki yanzu naki ki min addu'a na dawo lafiya na baki abinda kike bukata tayi shiru tana sauransa "may be mu dawo a cikin week din nan sai ki shiryawa karban takardan sakinki" "dana ji dadi wallahi dan har addu'a zan maka yayi murmushi yace "yanzu ma ki min addu'ar na dawo da raina da lafiyata sai na miki abinda kike so "to Allah ya dawo da kai lafiya sukayi sallama ranar da zasu dawo ya kira ta yace "yau zasu taso suna shirin zuwa airport , ya kira mumy ya fada mata tayi musu fatan alkhairi karfe bakwai suna zaune suna kallon labarai ita da zee aka nuno jirgin da zai taso daga amercan yayi cresh kuma babu wanda ya fita ciki ,gbdy hankali ya tashi dan zee sumewa tayi da taimako masu gadi aka kaita asibiti can gida ma mumy sumewa tayi tuni labari ya kai ko'ina mutanen unguwar su mumy sunji mutuwar muradi da Samir dady kuwa yafi kowa shiga tashin hankali lokaci guda ya sauya ya fita haiyacinsa aunty Ummi madu zee sai da suka sha ruwa jama'a da yan'uwa sai rarrashin Kisna suke a ganinsu rashin kukan da bata yi ba ba karamin illa zai mata ba nan gaba idan babu idanun mutane ita kuwa zuciyarta fesss take jinta ta rabu da alakakai cikin sauki ta huta babu mai tunhunarta akan rabuwarsu ,mumy ta kalli Kisna tana share hawaye ganinta har da kuruciya yasa take wasu abubuwa ana gobe za'a yi uku su muradi suka sauka a Nigeria su kuwa saboda haushin rashin zuwansu akwana uku da suka wuce Allah bai yi ba da aka gaya musu tafiyar tazo dan haka basu fadawa kowa cewar gasu nan zuwa ba , sun fi son sai angansu suna sauka muradi ya kira layin madu wayar a kashe motar campaign ta kawo su har gida sai dai abun mamaki babu masu gadinsu hasalima gidan a kulle yake nan take suka koma cikin motar suka bada umarnin akai su unguwar su mumy, yayinda kowannensu ke kokarin neman layin matarsa amman wayar na ring ba'a dauka ."...
suna shigowa unguwar suka ce me kuma akayi a kofar gidansu cunkushe da mutane fuskokinsu cike da damuwa tun kafin su isa mutane suka fara darewa wasu sun boye wasu kuma suka biyosu a baya a haka suka isa gaban dady shi dai dady bai ji tsoron ya'yansa ba ya rungumesu ajikinsa yana kuka mutanen gurin da sukayi zuru suna sauraron bayani muradi "eh babu mu acikin jirgin daya yi hadari sai kuma aka fara barka da fatan Allah ya kiyaye tuni labari ya isa cikin gida suka shigo falo suka iske su aunty ummi mufeeda Zahra har da afra ido ya canza saboda kuka ,da tsokana muradi ya matso kusa da mumy ya kwanta ajikinta "mumy kwantar da hankalinki ga muradinki muradin hjy kayi ya dawo gareki cikin koshin lafiya mumy ta share hawayenta ta kamosu jikinta gbdy ta rungumesu sannan ta kamo hannun muradi "Aliyu nah "ya amsa da " na'am uwata ta kaina " ta daga hannu sama tana godiya ga Allah daya dawo mata da ƴaƴanta lafiya muradi ya dubi aunty ummi yace "ki daina kuka haka baki rasa yan'uwanki ba jan kunnuwansu tayi "me yasa baku mana waya ba gashi duk layukanku a rufe muradi yace "Ni kin gane abun ne ya 'bata mana rai mun fito zamu hau wannan jirgin da yayi crash a she jirgin ya tashi mu bamu sani ba a cewar su bamu fito da wuri ba duk dai Allah yasa zaku fitar da zakkar hawaye ne jama'a unguwar sai shigowa taya mumy murna yaranta sun dawo lfy suke Kisna kuwa bakinciki kamar ta mutu murnarta ta koma ciki kana kallonta kasan batayi farinciki da dawowar muradi ba ta koma daki ta kunshe kanta ita kuwa zee gaban kowa ta rungume Samir ajikinta tana kukan farinciki dawowarsa lafiya ,bayan an gama murna mutane sukayita tafiya, gida ya rage daga su sai su muradi sai raba idanu yake yaga ta inda Kisna zata fito har kusan awa biyu bai ganta ba ya kasa hakuri ya kira aunty ummi a waya tana dauka yace "wai ina hjy kayi ne ?"baka ganta bane ?yace "eh "okay rike waya bari na dubota ta nufi dakinsu tana shiga ta isketa kwance akan gado tana baccinta na gado "gata bacci take bari na tasheta "ke Kisna ki tashi .."no ki barta kawai ya katse kiran .."
Tana kwance a dakin mumy bayan ta idar da sallah isha'i ya shigo dakin ya tsaya akanta yana kallonta gabansa na faduwa bacci take sosai dan rabin idanunta a bude suke wanda ke nuna alamun bacci take muddin idanunta na rufe kuwa ba bacci take ba tana jin duk abinda ake yi ,ya cigaba da kallonta yayi missing dinta sosai ya tsugunna a gabanta ya manna mata kiss a kumatu sannan yayi kasa da bakinsa zuwa lip's dinta haka nan yaji yana bala'in tausayin kanshi akan zamansa daita duk da ba wai sonta yake ba sai dai ta rigada ta zamo wani bangare na rayuwarsa ko ya rabu daita da wuya ta mantata a rayuwarsa , ya zauna a daidai cikinta tare da kamo yatsun hannuta cikin nashi yana murzawa a hankali yana kallon fuskarta for good 5 minti zuciyarsa na matukar bugawa a qalla ya kusan minti talatin zaune bata farka ba yayi mamakin yadda tayi nauyin bacci yau ya mike ya wuce sai kusan goma ta tashi ta sauko daga gado ta nufi bayi ta watsa ruwa tana tsaka da sa kaya ya shigo da sallama tayi saurin kare boobs dinta tana furta "wayyo Allah me kuma ya shigo yi ? "tayi saurin karasa saka kaya ya zauna idanushi na kanta gaba-daya ya kasa motsi yana kallonta ganin taki zama ya yafitota da hannunsa taki zuwa inda yake ta cigaba da tsayuwa , ya ɗan mike ya janyo hannunta yana cewa " tun dana dawo baki daura idanunki akaina ba koda yake nasan bakiyi farinciki da dawowata ba kou?
"gaskiya kusan haka ne amman tunda ka dawo din bai da matsala, tunda damuwata ta kusan zuwa karshe zaka min abinda na bukata tana gama maganar, jikinsa yayi sanyi matuka duk da yasan hakan zai iya fitowa daga bakinta amman yaji babu dadi a ransa bai sake cewa komai ba ya janyota jikinsa gabadaya ya rungumeta tare da matseta ajikinsa wani irin yanayi taji ajikinta gabadaya tsigar jikinta suka mike Numfashinta sai daya nemi ya dauke saboda faduwar gaba tasa hannu ta toshe hancinta da bakinta saboda kamshin turarensa daya kaiwa hancinta ziyara "i really miss you hajiya kayi " kokarin zame jikinta take daga nashi yayinda shi kuma yaki sankinta ya sake mata kyakkyawan riko cikin daukewar numfashi tace "Dan Allah kayi hakuri ka rabu dani haka banason kana rikeki ya sake matseta nan fa ta soma yunkurin amai ajikinsa kafin kace mai ta fara kwara masa amai ajiki bai katseta ba har sai data gama ya ɗauketa zuwa bayi ya taimaka mata ta wanke jikinta ya dawo daita daki yana kallonta "daman baki da lafiya ne?"kai kawai ta gyada masa alamun "eh "amman shine baki fada min ba maza tashi muje asibiti "
Ta kalleshi a kaukace sannan tace "babu inda zani naji sauki kamshin turarenka ne ya yau kaina da yawa "yayi shiru yana nazarinta cike da mamaki yaga