Showing 126001 words to 129000 words out of 495987 words
Chapter 43 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
chart ne . "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi za'a iya tuntu'bar Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos lace da kamfala ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da chiganvy, volyal lace duk akan farashi mai sauki ,ga mai bukatar siyan ɗaya ko sari yayi magana ta wannan number 08059623096,
....Kuka hajiya kayi ta fashe dashi tana furta kalmar "Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun tana sake maimaitawa jikinta na wani irin rawa , gabad'aya tsigar jikinta suka mike tsaye kanta kamar zai tsage gida biyu , wani ya dinga wani irin bugawar da bata taɓa jin irinsa ba saboda tsananin tashin hankali da kyar tasanyawa jikinta jarumta tace "yanzu ina shi baban yake "? Ta tambayi dicter hawayen tausayinta na zubo mata dan duk rashin imaninka sai ka tausaya mata muryarta cike da tashin hankali tace "Yana garin Abuja tare da wata yarinya Aysha data zo daga Lagos , gbdy idanunsa sun rufe akanta ba yaji baya gani sai abinda tace ni ba sonta da yake yi mata yafi damuna ba kamar yadda yaki amsar yaran ya'yan cikinsa "meye laifinsu da zai dinga nuna musu kiyayya ? "Idan ni baya sona su fa jininsa ne ta karasa maganar tana zubar da hawaye .
Hajiya kayi tayi shiru kawai tana sauraronta tana nazarinta cike da tsananin tausayawa yayinda dicter ke kuka sosai tana tausayawa yaranta dan sune abun tausayi yanzu "Allah ya kyauta Allah ya shirya mana zuri'a shiri na addinin musulunci ,Allah yasa ya gane ,Allah ya karkato min da hankalinsa zuwa gida murmushin takaici dicter tayi mai idanunta na zubar hawaye dan tasan wannan ɗan nata da take yiwa addu'a yayi nisan da bai jin kira, rayuwar duniya ce kawai a gabansa babu wani zancen dawowa gida dan tunda take dashi bata taɓa jin ya bukaci ganin iyayensa ko yan'uwansa ba shi dai rayuwa .."
Mike kafafu hajiya kayi tayi zuciyar sam babu dadi gaba-daya ta nemi natsuwarta ta rasa kawai zaune take amman ita kadai tasan Yadda take jin a zuciyarta "wai dan cikinta ya dawo haka "? Allah ya shirya ta sake furta wa a fili tana kwallawa Jamila kira "Jamila wai har yanzu bacci kike ? " Ki tashi munyi baki kusan kira uku tayi mata tana shafa kan aliyu sannan ta amsa tare da fitowa ta bi dicter da kallo da yaran kafin daga baya tayi musu sannu ta durkusa a gaban hajiya kayi dake cigaba da shafa Aliyu tunda ta daura idanunta akan yaran taji sun shiga ranta amman soyayyar Aliyu dabam taji a zuciyarta kwatankwacin wacce takewa ubansa ne saboda shine ya dauko komai na haroon dinta babu abinda ya bari " d'aura musu abinci Jamila tayi magana zuciyarta cunkushe da bakinciki saukinta ma mijinta baya raye da tasan tashin hankali da za'a fuskanta sai yafi wannan, dan bazai yarda da yaran ba , tunda ubansu ma ya haramta masa zuwa garesa bare wasu ya'yansa cikin sauri Jamila ta daura abinci dan ko ba'a fada mata su waye ba tasan suna da matsayi a gurin hajiya kayi bayan ta daura ta dawo ta tsaya tana jiran karin bayani kafin tace wani abu hajiya kayi tace "Kaita tayi wanka sannan kiyiwa yaran wanka kafin abinci ya nuna ta juya ta dauki botiki ta isa bakin rijiya ta cika botiki da ruwa ta nufi hanyar bayi "tashi rashida ki wasa ruwa kinji Allah zai kawo mana sauƙin lamarin ta mike tsaye ta bi inda Jamila ta shiga tana maganar zuci "wannan sunan ya zamo tarihi a rayuwata domin na bar muslinci har abada duk da ina tsananin son addinin musulunci amman dangina bazasu yarda ba ".
Jamila ta gama abinci ta zubo musu ta bar kwano a bude da miya ta kawo gabansu inda suke zaune akan tabarma kaba "ga abinci amman ku bari ya dan sha iska kunji ta fada tana kallon fuskar sadiq da Aliyu gyada mata kai suka yi sannan ta nufi gurin randar kasa ta zuba ruwa a buta tayi alwala ta soma ƙoƙarin gabatar da sallah itama Hajiya kayi mikewa tayi tayi alwala
Tana yiwa haroon addu'a a zuciyarta
bayan ta idar ta dade zaune tana addu'a da tunanin duniya .."
Bayan sun gama cin abinci sun huta Hajiya kayi da kanta ta sake yi musu wanka ta sauya musu kaya sannan tayi musu shimfida tare da kulla musu gidan sauro suka kwanta amman ita da dicter suka kasa kwanciya suna zaune yayinda hannu hajiya kayi ke rike da mafici tana su Aliyu fifita dan su samu damar runtsawa , shiru gidan baka jin motsin komai sai na tsuntsaye a hankali zuciyarta ke aiyana mata abubuwa da yawa , da akwai network a garin da babu abinda zai hana ta kira tillon diyarta ta sanar mata da halin da danuwanta yake ciki ,ta dinga jin kamar ta fice a daren taje inda suke samu network ta fara sheidawa yaranta maza sai dai wani bangaren na zuciyarta na gargadinta akan aikata hakan domin komai zai iya faruwa gara ita salaha zata fahimceta akan mazan dan matsalar mace sai mace ita zata kawo hanyar gyara saɓanin mazan , ranar dai bata samu isasshen bacci ba har gari Allah ya waye da safe itace da kanta tayiwa yaran wanka dicter da Jamila nacewa ta barsu zasu yi musu amman sam hajiya kayi taki sosai ta dinga basu kulawa da jikinta da aljihunta har sukayi kwana biyu suka saba daita sosai tana nuna musu kauna da kulawa fiyye da tunanin mai karatu har zuwa lokacin babu wanda ya san da zuwan dicter acikin ya'yanta sai Jamila hatta mutane gari basu san takamaiman abinda ya kawo dicter ba sai dai duk wanda yaga yaran sai ya dasa ayar tambaya akansu ".
Abunka ga kauye kafin kace me tuni an soma gutsiri tsoma cewar haroon yayiwa yarinyar ciki shege ne bata hanyar auren ba aka kawo wa hajiya kayi shegu yaran da aka haifar masa wannan kalmar itace tafi komai konawa Hajiya kayi rai ta dinga ji haushi mutane bisa rashin dalili sai dai babu yadda ta iya tunda tasan gaskiya suka fada , duk wanda ya tare da maganar kuwa cewa take karya ne ya'yan sunah ne ba shegu ba "..
Ranar da dicter ta cike sati biyu a kauyen ilo ta soma shirin tafiya benue sai dai zuciyarta tayi rauni sosai dan haka ta sanya yaranta gaba dake kwance akan gadon hajiya kayi tayi tagumi tana Kallonsu daya bayan daya, tsawon lokaci ta dauka tana Kallonsu cike da tausayawa sannan ta mike ta fito hannuta rike da jakar kayanta inda ta iske Hajiya kayi tsaye a tsakar gida zaune akan kujera ta karasa ta durkusa a gabanta muryarta a raunane ta soma magana "a yau zan bar garin amman ban san me zan ce akan zaman yarana agurinki ba ,sai dai na bar komai a hannun allah da hannunki dan nasan zakiyi abinda ya dace akansu ,a ɗan zaman da nayi dake na fahimci yadda kike son haroon Kuma hakan yasa kike jin qaunar yaran nan ina da tabbacin zaki so jininsa fiyye dashi da kika haifa amman duk da haka zuciyata na cike da rauni da alhinin rabuwa da yarana ta goge hawayen da suka gangaro bisa kuncinta sannan tasa hannu ta ciro farar envelope wanda tayi tanadinsa domin bata ,ta mika mata a matukar tsorace Hajiya kayi tace "menene haka kikeyi bazan amsa komai daga hannunki ba waɗan nan yaran dole na ne na dauki nauyin su, karki damu zan kula dasu kamar yadda zan kula da kaina, nayi na wasu ma da bansansu ba bare waɗan nan da suka kasance jinina kuma daga dan dana fi so a rayuwata, karki wulakantani ta hanyar bani waɗan nan kudaden da babu abinda zasu min sai karin bakinciki ".
"ba haka nake nufi ba Hajiya na fahimci yadda kike jinsu a zuciyarki , bana baki kudin nan dan kulawa da rayuwarsu bane , a'a wannan kudin nasu sadiq ne saboda zasu bukace siyan sweet da wasu abubuwan yara ki siyan musu abinda suke so daga hannun mahaifiyarsu dan allah ki amsa ki ajiye musu agurinki bani da wani abinda zan basu tayi maganar cikin zubar da hawaye ......"
"bafa zan amsa ba duk abinda suke so zan siya musu da kudina na faɗa miki zan yi musu komai muddin ina raye bai kamata ki damu ba tunda kema kinyi iyakar kokarinki akansu zai fi kyau ki ɗauki hanyar komawa saboda nisan dake tsakaninmu da inda zaki "shikenan na gode bari na shiga na sake dubasu ta ajiye jakarta ta bude ta dauko kyakkyawan diary dinta ta rike tana tunanin wa zata bawa acikin ya'yanta domin adanawa idan sun girma su fahimci halin rayuwar da tayi dasu a hankali ta juya ta soma tafiya zuciyarta na karfafa mata gwiwa akan ta bawa Aliyu har ta koma ciki d'akin zuciyarta na rawa da bugawa wanda zuwa lokacin tuni sadiq ya farka yana zaune a tsakiyar gadon yana tunani inda ta shiga ta barsu "kar dai mommy ta wuce ta bar mu anan ne "? ya fadi a haka fili hankalinsa a tashe dan shi sam baya qaunar zaman kauyen gara Abuja sau dubu agurinsa .."shigowarta yasa shi sauke numfashi yana dubanta, ta zauna a gefen gadon idanunta na kansa a hankali ya sauko daga kan gadon ya tsaya a gabanta yana yatsina fuskar ta kamoshi jikinta ta rungume tsam "fatan kayi bacci mai dadi yarona "?Shiru yayi yana jin wani iri ajikinsa " mommy kamar akwai abinda kike son faɗa min tun jiya "Yes I do my son naso na faɗa maka tun jiya sai dai fargaban halin da zaka shiga kai da kannenka ya hanani furtawa amman yanzu ya zama dole kasani ina son komawa gurin yan'uwana da mahaifiyata domin karasa rayuwata tare dasu zan yi haka ne saboda bani da wata damar data sauranmu baya ga komawa garesu tana cikin magana idanunta ya sauka akan Aliyu a she Shima ya Dade da tashi miskilanci ne ya hanashi mikewa ta kai hannu ta riko hannunsa cikin nata ta mikar dashi tare da kwantar dashi ajikinta tana shafa kwantaccen sumar kanshi mai taushi " sadiq kaine babba ka kula da kanka da kannenka ka dai ga irin rayuwar da mahaifinku yake yi da irin wahalar da muka sha a hannunsa, ka jajurce domin inganta rayuwarku zan dinga kawo muku ziyara lokaci zuwa lokaci zan so ka karfafa zuciyarka ta bambamta data mahaifinka , zaku cigaba da rayuwa anan tare da kakarku kuyi hakuri da rayuwa yarana ,zan barku anan ne ba dan bana sonku ba sai dan babu yadda zanyi amman zuciyata na cike da matsanancin damuwa akan nisan da zanyi daku abinda nake so daku ku cigaba da zama anan tare da kakarku zata kula daku zata soku fiyye da babanku ta karasa maganar tana rungunesu ajikinta tana jin kamar numfashinta zai bar gangar jikinta "mommy ni dai gaskiya karki barni anan gara ki maidani gurin babana ni ina son zama tare dashi tayi shiru tare da sausauta rungumar data masu ta tsura musu ido na wani lokaci sannan tace "kaima Aliyu kafin son zama da babanka akan grandma "?Yayi sauri girgiza mata kai alamun baya so "nafi son zama anan karki damu mommy kiyi tafiyarki kawai idan muka girma zamu zo har inda kike a kankara ya furta muryarsa a raunane " really my boy zaka zo gurina "?ya gyada mata kai alamun "eh "Idanunshi suka yi raurau alamun yana son yi kuka kawar da fuskarsa gefe yayi yana ƙoƙarin danne kuka ta juyo da fuskar gareta "tsaya haka yarona karka boye min damuwarka da kukanka "no mother karki damu dani I really want to you to go zan cigaba da rayuwa anan shiru tayi cike da tausaya masa dan tasan ya faɗa ne kawai dan karfafa mata gwiwar tafiya amman yana da kulafucinta sosai ba kamar sadiq ba wanda daman shi tana kallon tsantsar qaunar da yakewa mahaifinsa "ka gani ko sadiq kaninka ya fika wayo da hankali kuyi zamanku anan kunji yarana Allah yayiwa rayuwarku albarka karku damu zakuyi farinciki anan nima zan dawo gareku nan bada jimawa ba da zarar na koma bakin aikina alamura suka daidaita zan zo na maidaku inda nake ta karasa maganar tana fashewa da wani sabon kuka, suka soma rige rigen goge mata hawaye cikin tsananin soyayarta suna cikin wannan yanayin Hajiya kayi tayi sallama ta shigo ta ɗauki Nuhu dake bacci ta goya a bayanta tace "tashi ga mota can zata kwantagora sai kibita zai fi miki sauki ,babu mutsu ta mike tsaye jikinta na rawa suma jikinsu duk rawa yake ,hawaye na sake gangaro mata suka nufi waje da baya da baya ta dinga tafiya har ta bar dakin idanunta na zubar da hawaye kewar yaranta jikin yaran yayi mugun sanyi barin ma Aliyu da kana kallonsa zaka fahimci irin tashin hankali da yake ciki duk da ƙarancin shekarunsa suna kuka dicter na Kuka har da shesheka , Hajiya kayi ta rungumesu a jikinta tana rarrashinsu cikin harshen zarma dan tunda suka zo shi take musu yayinda mahaifiyarsu ke musu turanci , suka kamkame Hajiya kayi suna ganin mamansu zata shiga mota suka zare jikinsu da sauri suna Kallonta Aliyu kam kana kallon yadda yake janyo numfashi da ajiyar zuciya da kyar dan har kana iya hango tashin hankalinsa a makoshinsa dake lobawa yana tashi, hawaye na gangaro masa zuciyarsa cike da bakinciki kuma tun a wannan ranar ya dasawa zuciyarsa tsananin tsanar mahaifinsa a zuciyarsa bancin mugun hali irin nasa da zasu rayu tare da mahaifinyarsu koda kuwa bazasu ci bazasu sha ba kasancewarsu tare zaifi dacewa akan nesanta juna...
Dicter ta kamo hannu Aliyu ta saka diary aciki "kayi masa adani tamkar yadda kasan zaka adana mamanka duk runtsi Karka yi kuskuren rabuwa dashi domin shine rayuwar mahaifiyarka tana gama fadar haka ta juya ta shiga mota bayan ta zauna ta waigo tana kallon Aliyu dake zubar da hawaye ta daga masa hannu " gud bye ta furta masa a hankali "mommy zanyi kewarki sai dai zan yi kokarin ganin na girma da burin daukar miki fansar abinda mahaifinmu yayi miki kinyi hakuri matuka, kinyi komai dan ki rayu tare damu amman mahaifinmu yaki baki wannan dama "karka damu yarona just take care of yourself wasu zafafan hawaye suka gangaro mata ka girma da zuciya mai kyau da ƙoƙarin inganta rayuwarku kai da yanuwanka kada kazama loser irin mahaifinka I will try mommy karki damu zan zame miki yadda kike buri tana hawaye tana d'aga masu hannu suma suna d'aga mata hannu a hankali motar ta soma tafiya suka biyo motar da gudu suna kuka ta juyo tana Kallonsu tana sheshekar kuka "bazan taba yafe maka ba haroon tunda kayi sanadin rabani da farincikina tana kuka tana tsine masa ,na dinga tsine maka kenan a dukkanin shafukan rayuwarka nadama da danasani zaka yisa a lokacin da nadamar bashi da amfani , sai rayuwarka ta kaskanta a duniya sai kaga kudi kace kashi da yarda Allah sai kazama abun tausayi a idanun duniya har ta isa benue hawaye bai daina zuba daga idanunta ba tana shiga gidansu da mahaifiyarta ta soma cin karo a parloun zaune tana ganinta ta mike jikin ta na rawa ta rungumota jikinta tare da zaunar daita "daman zan sake ganinki dicter?" A she idanuna zasu sake ganin sanyin idaniyanta ? Ina yaranki suke ? kuka take sosai a jikin mahaifiyarta batare da bata amsa ba "taso muje ciki diyata mai ya faru da dake haka ina yaranki suke ta sake jeho mata tambayar zaunar daita tayi a bakin gado har lokacin kukanta yaki tsayawa "hankalin mumy ya tashi " ki faɗa min idan wani abu ya samesu ne ......"?Cike da Muryar kuka tace babu abinda ya samesu na maidasu gurin dangin ubansu na dawo gareku kamar yadda kuka bukata naunayen ajiyar zuciya mommy ta sauke ta sake rungumeta duk da bata ji dadin hakan ba ,cikin kankanin lokaci y'an'uwanta suka samu labari ta maida yaran sunyi murna kamar waɗan da akayiwa albishir da rabin duniya washegari gari aka gyara mata d'akinta komai sabo aka saka mata ema ya amshi takardunta "kina son cigaba da aiki a inda kika fara ko a canza miki "?
"Duk yadda kukayi ta fada zuciyarta na tsinkewa cike da jin haushinsu a ranta dan duk abinda zasuyi mata ba zai saka zuciyarta farinciki ba kuma baya gabanta kuma bazai burgeta ba ."
******
Tunda dicter ta komai gidansu bata samu kwanciyar hankalin da take bukata