Showing 270001 words to 273000 words out of 495987 words
Chapter 91 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
bayan bayanin malamin bai baku wani abu kunci ba "? "babu idan mun taba yi kinsan zan faɗa miki ",to kun taba shan jinin juna ? Kisna tayi shiru tana tunani dan tasan sun taɓa sha "kun taba sha ko ? Kisna ta gyada mata alamun" eh "subuhanallahi shiyasa kuka kasa rabuwa da juna wallahi " dan Allah aunty afra ki taimaka min na auri musa sannan ki taimaka kije min gidansu ki duba min shi wannan azalumin yayi masa dukan mutuwa ko ina ruwansa da rayuwata ?
"Abinda Aliyu yayi masa daidai ne baki ga har kalazir musa ya watsawa mumy ba ke yanzu zaki iya auran mutumin da ya iya watsawa mahaifiyarki kalanzir har yana cewa a bashi a shana suka jiyo Muryar mufeeda a bayansu ."Wallahi ban taba jin na tsani wani halitta a rayuwata ba kamar yadda na tsani ke da wannan yaron ,ke ko mu da ba mumy ce ta kawo mu duniya ba bazamu iya ganinta cikin damuwa ba bare ke wallahi ki guji fushin mahaifiyarki idan nan gaba duniya ta juya miki baya Allah yasa muna raye mu karar da abinda kika shuka da karanshin shekarunki yar banza yarinya kawai mara imani ta k'arasa maganar tana barin dakin ...
Kisna ta rushe da kuka "kowa ya tsaneni a gidan nan ,me yasa bazu fahimceni ba? "Karki damu ki kwantar da hankalinki zan san abunyi afra na gama fadar haka ta mike ta bar dakin tare da kullewa kamar yadda suka iske ta kaiwa mumy key ta nufi bangarenta a lokacin ya badamasi na zaune akan kujera ya daura kafafunsa akan center table yana tunanin matsalar kisna da taki ci taki cinyewa , Afra ta karasa shigowa ta zauna "baby Ina son magana mai mahimmanci da kai ya waigo ya dubeta tare da cewa "uhmmm ina jinki "daman akan maganar kisna ne da yaron nan ,yadda kuka ɗauki lamarin yarinyar nan ya wuce haka, mai zai hana ku hakura ku barta tayi soyayyarta da yaron nan ya badamasi karkata kai yana Kallonta cike da mamaki jin maganarta "yadda kuke ganin aibunsa ita fa bata ganin hasalima bata ganin makusansa ku barta tayi soyayyarta har sanda zasu auri juna idan Allah ya kaddaro hakan shi fa so babu ruwansa da wani kudi ko galihu ko yare ko addini ko kankata tunda ta soma magana yaji wani abu ya tokare masa makoshi , ya jima yana mamakinta kafin daga baya ya soma magana cikin fushi "ke yanzu ina ruwanki da matsalar gidanmu ? "Idan dai wannan ne gudumuwarki garemu to mun yafe dan Allah ki adana shawararki ko zai miki amfani a wani guri amman agurinmu bashi da wani amfani ,
kuma karki sake zuwa min da makamanciyar wannan maganar idan ke baki da hankali mu muna dashi mu rasa wanda zamu dauki kanwamrmu mu bawa aure sai wannan tantiri kuma dan shaye shaye wallahi gara ta mutu mu binne gawarta akan mu barta ta auri yaron nan ,karma kiyi kuskuren faɗar wannan shawara taki a gaban Samir ko Aliyu Dan zasu miki abinda bakiyi expecting ba ,ya mike ya shige daki ya barta sake da baki tana kallon kofar daya shiga " a she akwai sauran kallo a gidan nan kenan tunda bazaku dauki shawara ba ,kuma kuna tare da aiki dan yanzu kuka fara ganin bala'in , ni meye nawa daga bada shawara za'a nemi cinyeni ? Kowa yaji da damuwarsa ni tawa damuwar ma ta isheni ta mike ta shige d'akinta ."
******
A daren wata ranar talata bayan dady ya idar da Sallah isha'i yana zaune yana addu'a kuka ya tsarkeshi ya kasa ci-gaba da addu'a yana cikin wannan halin aka turo kofar dakinsa aka shigo muradi ne a gaba sai Samir dady yayi hanzarin tashi zaune yana kokarin mayar da kukansa ciki tare da sanya hannu yana goge wanda ya bata masa fuska cikin dabara wai dan karsu gane amman ina tuni muradi ya fahimci kuka yake dan suna hada ido dashi sai jikinsa yayi sanyi kuzarin jikinsa ya sake yin kasa ya tsani yaga dady ko mumy suna zubar da hawaye akan matsalar kisna cikin tsanye jiki ya koma ya jingina bayansa da bangon dakin yana ma dady kallon tausayawa cikin tsananin damuwa Samir yace "plz dady me yasa kake hasarar hawayenka dan Allah ka bar komai a hannunmu zamu yi iyakar kokarinmu cikin kakalo murmushin dole dady ya fito muradi yana cewa "zo nan dana kai kuma wa ya fada maka kuka nake yi ?muradi ya karaso ya kai hannu a idanun dady yana goge masa guntun hawaye da bai rigada ya goge ba tare da cewa ",ga hawaye nan a idanunka sannan idanunka sunyi ja dan Allah dady kuyi hakuri wallahi kullum cikin tunanin mafuta nake akan matsalar nan banaso wani abu ya taba lafiyarku akan wannan matsalar Samir ya ja doguwar ya zauna suka tasa dady gaba suna kwantar masa da hankali dady ya sake kurawa yaransa ido da suka dawo kalar damuwa adalilin nashi damuwar "na fada muku ba kuka nake ba ......"
Manage not edit 👏🏼
Mmm Sudais
[7/19, 5:32 PM] +234 803 631 5951: 💗💗💗💗💗💗
CUTAR DA KAI
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Page 39
~TRUE LIFE STORY~
*PAID BOOK*
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
"Wannan littafin na kudi ne ,mai bukata karanta shi zai tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number alert +234 803 238 4602 domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne . "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi za'a iya tuntu'bar Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos lace da kamfala ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da chiganvy, volyal lace duk akan farashi mai sauki ,ga mai bukatar siyan ɗaya ko sari yayi magana ta wannan number 08059623096.
......Idon muradi ya cicciko da ruwan hawayen tausayin dady saboda ganin yadda dady yayi shiru tare da tsura musu idanu wanda yake nuni daya cikin tsanani damuwa sai dai yayi dabara ya mayar dasu yana cewa "ka sani dady rayuwa na tafe ne da jarabawa kala kala kuma hakan ba yana nufin Allah ya manta da kai ba ko baya sonka bane sai Allah na sonka ma sannan zai jarabeka sannan cikar imaninka zai cika, kowane mumini ya yarda da qaddara mai kyau da akasinsa sannan dady zababbun mutane ake jarraba kada ka sanyawa zuciyarka damuwa da yin Allah damuwar da zai taba imaninka kayi hakuri inshallahu Allah ba zai bar rayuwarta haka ba muddin muna duniya baza mu bari ka cigaba da kuka akanta ba, ita kanta nan gaba zatayi ingantacciyar rayuwa a duniyarta da izinin Ubangiji amman halin da kuke jefa kanku kai da mumy a sanadiyyarta yana bala'i d'aga hankalina dana Samir ka taimakemu dady ka cire damuwar nan koda ba duka ba kaci abinci domin ka samu karfin jikin da zaka yi addu'ar nemammata shiriya a gurin Allah dady ya daure zuciyarsa cikin jinjinawa d'ansa muradi wanda samun d'a irinsa ke da matukar wahala a wannan lokacin sai an tona ma kafin a samu ,yana matukar son shi gashi dai shi din daga wani tsatso ya fito wanda har lokacin babu tabbaci akan mahaifiyarsa sannan babu nagartaccen uba na gari sai shi daya dogara dashi wannan shine matacce ya fitar da rayayye ina ma zai amshi auren kisna a wannan halin da suke ciki wallahi da babu abinda zai hana bai aura masa ita da karancin shekarunta dan yasan shine mutumin da zai kula daita da rayuwarta sannan zai sota da irin tawayarta da lalurarta na rashin jin magana ,sai dai ina kowani rai yana son abu mai kyau ko ɗan iska yana son natsatse ba dan iska dan'uwansa ba kar ta zo tana bashi ciwo kai , a hankali ya dinga tunanin wanda zai bawa auren kisna ko a cikin danginsa ne , zai nemi alfarma agurin ahlinsa su rufawa juna asiri sosai dady yayi zurfi cikin tunani kafin daga bisani sautin muryar muradi ta dawo dashi "Plz dady ka daina dogon tunani haka zai iya shafar lafiyarka "inshallahu na daina d'ana daga yau zan rage muradi yaji dadi sosai har da murmushi yace "na gode dady sai ya janyo kular abincin da'aka kawo masa mai cike da lafiyayen abinci ya bude cike da girmamawa "Bismillah dady ka daure kaci abinci a hankali shi da samir suka dinga lallaba dady har yaci abinci yana ci yana kallonsu tare da alfahari dasu ..."
Da misalin karfe goma na daren ranar afra na kwance akan makeken royal bed dinta ita kadai kasancewar ya badamasi na gurin aiki bai dawo ba sai zuwa shadaya , gabad'aya ta nemi natsuwarta ta rasa ji take kamar zuciyarta zai buga akan tsananin tunanin muradi juya kai kawai take zuciyarta na sake harzuka kamar ta daura hannu aka ta saka kuka ko taji sauƙin zafin da take mata
ta tashi ta zauna ta janyo pillow ta rungume a qirjinta tana jin tamkar shi ne a qirjinta tana cigabanani da nazarin hanyar da zata shawo kan muradi cikin sauki batare daya bata matsala ba sannu a hankali ta yarda da wasu daga cikin shawarwarin da zuciyarta ta bata dan haka a hankali ta mike ta zira silipas dinta ta fito cikin sand'a ta shiga parlour'n mumy taci sa'ar babu kowa sai karar tv dake aiki dan haka ta sanyawa jikinta kuzari da jarumta tayi hanyar step ta karasa jikin kofar dakinsu har zata yi knowcking sai ta fasa ta murda handle din kofar ta shiga ta maida kofar ta rufe har da murda key bata iske kowa a parlour'n ba dan haka ta kutsa cikin uwar daka anan ta hango shi kwance tayi shiru na yan mintina tana kallonsa kwance sanye da farar singlet da farin wando iya cinyarsa kallon kuralla take masa kamar zata cinyesa shi kuwa gogan da bai san da shigowarta ba sai faman aikin shafa qirjinsa yake yana lissafin shafukan rayuwarsa data gabata tamkar a mafarki ya ganta tsaye tana kallonsa ya zabura ya mike zaune gabansa na wani irin faduwa "Me ya kuma ya kawoki dakin nan maza maza ki kama hanya ki fita tun ban miki rashin mutunci ba kina son ki sani cikin bala'i ko me kuke nufi dani ?"na rokeki karki yi sanadin da zamu samu matsala da dan'uwana "I don't care about that da ku samu matsala da karku samu wannan ba damuwar afra bace damuwar afra ta samu gurbi a zuciyar Ali saboda soyayyar Ali ta rigada tayiwa rayuwarta kamun kazar kuku idan babu shi bazata iya cigaba da rayuwa ba "ai kuwa sai dai ki kare rayuwarki a haka dan har abada nayi miki nisa ke ko matan duniya kaf sun kare sauran ke afra wallahil-azim bazan yi rayuwa dake ba "ni kuma gashi burina mu rayu tare ba har ma na haifa maka kyawawan baby's masu matukar kama da kai ta kara taku biyu zuwa inda yake batare da wani tsoro ko fargaba abinda zai faru ba suna fuskantar juna "ina sonka gadanga dan nasan you so different daga cikin tarin mazan duniya kana da kamalawa da kamewa forget all the ..... "Yayi saurin katseta yana ja baya saboda kusancinsu yayi yawa dan har yana iya xukar numfashinta a hankali ya furta "azubillahi mina sheidanir raji saurin zaro ido waje tayi "ni kakewa uziyya ?"tayi maganar cikin tsananin fushi tana nuna qirjinta "fiyye da haka ma zanyi saboda kin zama sheidaniya "tunda kace haka kuwa tabbas zan tabbatar maka da hasashenka wait lemme prove it to you unexpected yaji ta zubo jikinsa gabad'aya ta rungumeshi tana kokarin hade bakinsu guri daya yayinda hannunta daya ke daidai gefen fuskarshi dake kwance da kwantaccen suma sai sheki suke zubawa saboda gyara saurin kawar da bakinsa yayi yana zaro idanunsa cike da matsacinan mamakinta bai dauka isksncinta ya girmama haka ba a hankali ta soma shafa gefen fuskarshi tana tura masa brest dinta cikin zafin nama ya hankadata tayi wani irin juyi tayi baya taga taga sannan ta tsaya bisa kafafunta tana kamkame jikinta guri daya idanunsa da suka sauya kala yake kallonta dasu tana son ta sake matsowa garesa sai dai hakan ya faskara saboda tsoron daya ziyarceta, numfasawa yayi cikin tsananin fushi ya nuna mata kofar fita daga dakin batare da yace uffan ba dan ko yace zai yi magana bazai iya ba saboda zuciyarsa tazo wuya ita kuwa afra tana nan tsaye kamkame da jikinta tamkar gunki tana kallonsa tamkar mutum mutumi haka ta koma saboda tsananin tashin hankali kusan minti goma daya ɗauka yana nuna mata kofar fita sai dai ita din ta kasa kwakkwaran motsi wani irin ajiyar zuciya take sauke tana jin duniyar tayi mata zafi dame yake son taji da shi son dake azabtar daita ko kuma da wulakacinsa suna nan tsaye suka ji ana buga kofar dakin da karfi shiru dukkaninsu sukayi kafin daga baya muradi ya kewayeta ya fito zuwa falon inda Samir ke sake kwankwasa kofar yana cewa "muradi ka bude min kofa me kake yi ne ka kulle kofa ? Yayi shiru haɗe da juyowa zai koma dakin sukayi karo da afra yayi saurin ja baya yana kakkabe jikinsa da hannu muryarsa a fusace yace "sai ki san yadda zakiyi da kanki dan duk abinda kike nufina dashi da yarda Allah kanki zai koma bai yi shiru ba ta soma magana cikin sanyi murya ta yadda daga ita sai shi zasu ji "bana nufunka da komai Aliyu sai alkhairi ka yarda dani sannan ka yarda zaka aureni na kashe aurena ko kuma muyi soyayya "wannan ne kuma bazaki taba samu ba har duniya ta nade ko kinga nayi miki kama da irin wadan nan yan iskan mutane ?"tun wuri ki san yadda zaki yi ki bar dakina tun baki jefa kanki cikin matsala ba "I don't care about that matsala ko wani ya ganni anan zai barni ya wuce babu inda zani ta karasa maganar tana sake jin wata irin zafafan soyayyarsa na taso mata tun daga cikin kasan zuciyarta tana jin kanta in har babu shi a rayuwarta tabbas mutuwa zatayi a hankali ya juya ya fara tafiya cikin zafin nama domin komawa cikin dakin tamkar bashi da laka dan ya lura afra nemanshi take da bala'i yayinda Samir ke cigaba da buga kofar ya zube akan katifa idanunsa na ganin duhu babu abinda zuciyarsa take sai faman bugawa baya son wani tashin hankali a rayuwarsa a bar da yadda rayuwarsa ke tattare da cuwuka kala kala har kusan shabiyun dare yana kwance bai sanda afra ta bar d'akin ba da shigowar Samir tun daga lokacin muddin yasan shi kadai ne a dakin zai kulle ...."
******
Kullum kisna bata da wani aiki sai na tunani yadda zatayi ta fito daga d'akin ta bar rayuwar gidansu gaba-daya ta huta da takura
a wani shigowa da ya badamasi yayi dakin ne yace suje asibiti a duba lafiyarta saboda ramarta tayi yawa gashi duk abinda taci sai ta amayar da kyar ta mike tsaye ta zira hijab dinta ta soma d'aga kafafunta iska na dibarta saboda rashin kuzari a bakin motarsa yace ta tsaya saboda ganin baba mai gadi zaune ya shiga bangaren mumy ya sheida mata , tayi masa addu'a muradi dake zaune kusa daita gaishesa yace "yaya bari na mike muje tare "mumy tace "a'a ka zauna ga breakfast za'a kawo maka bai so karyawa mumy gwiwa ba amman dole ya bata hakuri dan sam hankalinsa bai kwanta ba dan yasan ya badamasi da sakaci za'a iya neman kisna a rasa muryarsa a sarke yace "mumy kiyi idan na dawo naci nafi son nabisu Kinga idan ya gama daita sai mu dawo tare ko a motar haya ne basu tsaya bata lokaci ba suka fito tare ya badamasi na gaba muradi yana biye dashi cikin jc wando da riga yellow mai ratsin baki Suna fitowa falo ya bawa masu aiki umarnin gyara dakin da kisna take killace sannan suka sa kai suka fice tana nan tsaye a jikin motar rungume da hannuwanta kallo daya tayi musu ta dauke kanta tana tsinewa muradi dan babu ranar da bata tsine masa akan abinda yayi wa musa wanda har lokacin bata san a wani matsayi yake ciki ba yana raye ne ko ya mutu ya badamasi ya danna key din dake rike a hannunsa sannan ya bude mazaunin direba ya shiga shiru tayi ta cigaba da tsayuwa har sai da yayi mata magana a fusace "ki shiga mana kin wani tsaya dan rainin hankali kina kallon mutane jiki a sanyaye ta bude gidan baya ta shiga ta zauna tana daddaure fuska tare da shan kamshi sannan ta kawar da fuskarta gefe tana kallon glass din motar ko shigarta mota bai sa ya badamasi ya daina zazzaga mata ruwan maseefa ba kasa muradi yayi da murya yana cewa "haba ya badamasi ka bita a hankali dan Allah ku daina nuna tsanarta hakan zai sake tunzura zuciyarta "zuciyartata ta dade bata tunzura ba itace zata kare rayuwarta cikin wahala har suka karasa asibitin bata kalli inda suke ba haka zalika ya badamasi bai daina magana mai kamanceceniya da nasiha ba ."
bincike farko ya badamasi ya tabbatar da lafiyar kisna lau tsabar damuwa ce kawai tayi mata yawa da rashin cin abinci tana zaune akan daya daga cikin kujerun dake office din yayinda muradi ke zaune akan gadon duba marasa lafiya rike da waya yana danne danne wanda zaka ɗauka wani abu mai mahimmanci yake nan kuwa game yake bugawa sai dai gabad'aya hankalinsa na kan kisna duk motsinta yana hankalce dashi wanda zaka dauka sonta yake dan a fili yake nuna kulawarsa gareta,