Showing 81001 words to 84000 words out of 495987 words
Chapter 28 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
bawa aryan abinci , kasa zama kisna tayi ta biyo byn mumuy domin son aiwatar da kudirin ta .."
A tsakiyar dakin mommy ta iskeshi yana ƙoƙarin cire rigar jikinsa jin motsin shigowa dakin yasa ya juyo yana zare rigarsa ya saura daga shi sai farar vest da dogon wando a hankali ya shiga fifita da rigarsa yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa yayinda hannunsa daya ke rike da kugunsa sai zufa yake yi ,jijiyon kanshi duk sun mika sun yi rudu rudu tamkar wanda ya shiga fagen yaki " bana ce kabi komai a hankali ba me yasa zaka ........."shigowar kisna ya katsewa mumy hanzari ,kisna ta karasa shigowa jikinta a sanyaye idanunta na kanshi a kallon da take masa ta fahimci yana cikin tsananin damuwa "to me kuma ya sameshi"? tayi Maganar akasan ranta tana takowa inda jug din ruwa yake ta tsiyaya a glass cup ta karaso inda yake yana fidda numfashi ta mika masa kin amsa yayi sai da mommy tasa baki sannan ya amsa sai dai ya kasa kai cup din bakinsa yana jin tamkar ya saki cup din kasa ,babu zato babu tsammani suka ga ya matse glass cup din a hannunsa take cup din ya soma tarwatsewa ruwa da fasassasun glss suka yi kasa kisna da momy suka tsura masa ido hankalinsu a tashe cikin tsananin tashin hankali mumy ta rike hannunsa tana furta "menene haka muradi zaka kashe min kanka ne kalli yadda ...ai ganin jini ya fara diga yasa mumy yin shiru tare da rudewa cikin tsananin soyayya ta tsinka masa marin da sai data ji saukansa a zuciyarta kana da sauri ta yaga gefen zaninta, kisna ta matso kusa dashi tana kokarin taba hannunsa ya dakatar daita da hannunsa sannan ya runtse idanunshi gam dan baya son ganinta bai ji zafin marin da momy tayi masa ba illa gyara tsayuwarsa da yayi cike da jarumta, ahankali ya dinga motsa labbansa yana furta kalmar "kiyi hakuri momy kiyi hakuri ...." "karka sake cewa zakayi wani abu kaji na faɗa maka ka manta da komai "no mommy "no I can't ",wallahi mommy abinda Kika faɗa min nayi banyi wani abu dana san ba daidai ba ".muryarta a raunane tace "mommy me yasa mesa dan Allah kice masa ya dinga sawa zuciyarsa salama ya dinga bin komai a hankali idan wani abu ya sameshi ban san yadda su aryan zasu ji ba ......."
"har ke kanki zakiji babu dadi dan duk abinda ya samu uban ya'yanki ya sameki "a hakan da bai daukeni da daraja ba , bai san mahimmancina ba ,sannan bai damu da damuwata ba tayi zance a zuci "shima kuma bazai so wani mummunar abu ya sameki ba amatsayinki na matarsa kuma uwar ya'yansa inji cewar mumy , aliyu ya sake runtse idaunshi yana ciza gefen lip's d'insa da karfi mumy ta kamo sa ta zaunar dashi akan kujera "karka sake min irin wannan ganganci dan rayuwarka nada matukar muhimmancin gareni ta kalli inda kisna ke tsaye "kin wani tsaya kina kallon mu ki je dakina ki dauko min akwatin first aid ,juyawa tayi a sanyaye ta bar d'akin ko cikakken second biyar bata yi ba ta dawo ta ajiye ta sake fita dan dauko tsinyaya ta gyara gurin ta cigaba da tsayuwa tana kallonsu dan ko tace zata taimaka masa bazai yarda ba
mumy ta bude laulausan tafin hannunsa gabanta na wani irin faduwa ,shiru tayi tana kallon raunin daya ji ,tausayinta ya kamata taji kamar ta cire ciwon ta dawo dashi jikinta wanke masa hannu tayi da hydroxy da auduga, tana wanke raunin tana duba ko kwalba ya shiga naman hannunsa .
Bayan ta gama ta rufe akwatin ta janyo kisna tare da zaunar daita gefenta bayan kamar minti goma " kisna taga gara ta aiwatar da nufinta tunda gasu tare , ta kira sunan mumy a hankali "mumy ina neman wani alfarma agurinki saboda kece mutun ta farko a duniya da kike son zamana da ya Aliyu tun ada can baya har zuwa yanzu ,sai gashi har yanzu babu wani cigaba a rayuwar aurenmu.
"da cigaba mana me yasa zaki ce haka "? Mumy tayi mata tambayar a dan kufule dan yaji haushin maganarta "allah babu wani cigaba mommy saboda har yanzu ya Aliyu bai daukeni a matsayin matarsa ba me zai hana mu saukakawa juna ya sawakemin idan zaki wuce na biki mu koma tare dan wallahi zuciyata ta gaji da wannan zaman idan kuma hakan bai samu ba wata rana labarin mutuwa zai riskeku a lokacin da kuke tsananin bukatata ta karasa maganar hawaye na gangaro mata mumy ta damki tsintsiyar hannunta jikinta na rawa numfashinta na barazanar daukewa "ki kwantar da hankali mumy Allah rabuwar mu zai fi kwantar miki da hankali zucoyoyinmu zasu fi samun natsuwa Allah ya raya mana su Aryan "abinda ta faɗa gaskiya ne mumy nima ina iyakacin kokarina naga cewar na manta baya na inganta relationship din sake tsakaninmu amman na kasa idan dai har zai yiwu mu sawakewa juna ......."
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un " mumy ta shiga furtawa jikinta na tsananta rawa ..."
Inshallahu ku saurari 14 zuwa an jima
Mmn sudais
[7/19, 5:32 PM] +234 803 631 5951: 💗💗💗💗💗💗
CUTAR DA KAI
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Free page 14
~TRUE LIFE STORY~
*PAID BOOK*
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
"Wannan littafin na kudi ne ,mai bukata karanta shi zai tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number alert +234 803 238 4602 domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne . "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi za'a iya tuntu'bar Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos lace da kamfala ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da chiganvy, volyal lace duk akan farashi mai sauki ,ga mai bukatar siyan ɗaya ko sari yayi magana ta wannan number 08059623096,yauwa har ma da agwalumar cotonou mai dan Karan zaki muna turawa kowani gari ...🥰🥰
....Wani irin kyarma jikin mumy yake batare da sun fahimci haka ba saboda idanuwansu daya rufe, sai faman ya'bawa juna bak'ar magana suke cikin kunar rai ,
A matukar fusace Aliyu ya katsewa kisna hanzarin "na fiki son rabuwa dake mumy nima na amince da tsarinta mu rabu kawai kowa ya huta , dan Allah mommy ki sanyawa zuciyarki salama kiyi hakuri ki bari mu bar rayuwar juna mu cigaba da zumuncinmu shima idan zai yiwu idan kuma bazai yiwu ba kowa ya kama kansa ya fada yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa , wannan maganar data sake dokan kunnuwan mumy yasa taji wani mummunar faduwar gaba ya sake ziyartar jikinta , qirjin mumy ya dinga baguwa da tsananin karfi , duk wani tashin hankalin da take kokarin dannewa acikin zuciyarta sai daya fito fili saboda babu abinda ta tsana a rayuwarta kamar taji maganar rabuwa a bakin Aliyu dan na kisna mai sauki ne tunda sakin ba a hannunta yake ba ...."
Aliyu ne ya fara lura da yadda jikin mumy ke karkarwa kamar mazari yayi saurin rikota cikin tsansnin tashin hankali yana kiran sunanta "mumy !mumy!!! dan girman Allah mumy ki kwantar da hankalinki ".a hankali ta kai hannu ta dafe daidai qirjinta da taji yana mata wani irin zafi da bugawa " Please Karki min haka wallahi bana son na rasaki bana son wani abu ya sameki a dalilin rabuwata da kisna idanunta suka fara rufewa sakamakon kalmar rabuwar daya sake maimaitawa "mumy Please ki tamaineni ki bude idanuki me kike so ayi yanzu ? " duk abinda kike so a shirye nake zan miki matukar zai sakaki farinciki cikin tsananin tashin hankali kisna take furta mata haka kafin daga baya Aliyu ya kwantar daita akan katifa ya mike cikin sauri gaba-daya ya rud'e ya gigice hawaye sun cika masa kwarnin idanunshi tamkar ba wannan Aliyu mai karkarfar zuciya ba ya fita daga d'akin , itama kisna hankalinta yayi matukar tashi dan kusan tafi shi shiga tashin hankali, take ta fara data sani maganarta da bata furta kalmar su rabu da mumy bata shiga damuwa ba ,wani sabon hawayen ne yazo idanunta ya fara zuba akan kuncinta tamkar an bude fanfo , a hankali ta fara rera kuka mai ban tausayi ,ta sake riƙe hannun mumy dake cikin nata gam yayinda hawayenta yaki tsayawa sai faman kuka take da kiran kalmar "na shiga uku cikin tsananin tashin hankali "mumy na tuba bazan sake ba, bazan sake furta kalmar rabuwa da ya Aliyu ba tunda bakya son rabuwarmu , " ki taimakeni dan Allah karki mutu ki barni a gurinki kawai nake samun farinciki da kwanciyar hankali idan kika mutu kika barni rayuwa zata min muni, sosai take kuka tana rike da hannun mumy itama mumy ta rike hannunta gam hawaye na gangaro mata ... ....."
Zuciyar Aliyu na matukar zafi ya dawo d'akin hannunsa rike da goran ruwa bai tsaya tsiyaya ruwan a cikin cup ba ,ya ɓalle murfin goran da karfi wani zafi yaji ya ratsa tafin hannunsa inda yaji ciwo sai dai bai tsaya kallon tafin hannunsa ba ,ya soma shafa ruwa a fuska mumy yana kiran sunanta , naunayen ajiyar zuciya ta sauke sannan ta dinga sauke numfashi a hankali a hankali "sannu mumy suka hada baki gurin furta mata haka da kyar ta gyada musu kai idanunta na runtse ,Aliyu ya kamo kanta ya kai goran ruwa bakinta "ki sha ruwa mumy " .
Ta girgiza masa kai alamun bazata sha ba "dan Allah mumy ki rufa min asiri ki kwantar da hankalinki ya kalli kisna da idanunsa da suka rikice suka canza kala tamkar garwashin wuta ya soma magana cikin zafin rai "wallahi Idan wani abu ya same mumy a dalilin furucinki bazan taba yafe miki ba , kuma wallahi bazan cigaba da zama dake ba dole na yakiceki ta karfin tsiya daga jikina domin nafi bukatar rayuwa mahaifiyata akanki ya karashe maganar yana wurgi da rabon ruwa ......."
kuka kisna take sosai tamkar ranta zai bar gangar jikinta tana rike da hannun mumy Sun yi matukar tausayawa halin da mumy take ciki , bazasu iya daukar halin da zata shiga a dalilin cikar burinsu ba .......
Aliyu ya mike da hanzarin zai fita daga dakin domin kiran Samir dan sukai mumy asibiti ta rike hannunsa ya dawo da sauri ya daura hannunsa akan nata tare da zubawa mata idanunshi kamar zai yi kuka "mumy zanje na kira Samir ne mu kai ki asibiti" sake girgiza masa kai tayi ta zuba masa ido cikin sarewa tace "karku wani kai ni asibiti alhalin magani na gida , kune damuwata muradi , idan zanganku cikin farimciki da kwamciyar hankali wallahi nima zan kasance haka"bazan taɓa yarda da tsarinaku ba ,rabuwarku wani babban tashin hankali ne gareni bansan me yasa nake son kasancewarku tare da juna ba amma kafin na cigaba da magana ku amsa min wannan tambayar "?
ta soma yunkurin mikewa zaune daga kwance da take jikinta na daukar zafi Aliyu da kisna suka kai hannuwansu da sauri domin taimaka mata hannun Aliyu ne ya riga na Kisna sauka a gadon bayan mumy sannan hannunta ya sauka akan nashi saurin kallon kwayar idanun juna suka tare da jin faduwar gaba mai tsanani zuciyarsu ta dinga bugawa a tare , zuwa wannan lokacin ko'ina ajikin Aliyu rawa yake yayinda zuciyarsa ke dokawa da sauri sauri fiyye dana Kisna , gabad'aya gabobin jikinsa sun yi sanyi, a hankali Aliyu yayi saurin janye kwayar idanunsa a kanta itama tayi kokarin dauke hannunta dake kan nashi suka yi shiru a tare suna satar kallon kwayar idanun juna ,karamin bakinta ta turo masa tana kashe masa idonta d'aya ..
abinda tayi ya bala'i bashi haushi sosai and he don't want any dilemma with her ko sake kallon inda take bai yi ba dan gani yake bata damu da halin da mumy take ciki ba kukan munafurcinta data saba ne ...
Cikin sanyin jiki ya kamo hannu mommy cikin laulausan tafin hannunsa tare da matsowa gefenta sosai itama kisna ta sake matsota suka sakata a tsakiya ya d'ago kanshi a hankali ya watsa mata harara itama batayi sanya a gwiwa ba ta mayar masa tana murgud'a masa baki yaji tamkar ya buge mata baki ko janyo ta ya yaryarfa mata maruka masu rai da lafiya sai dai ya kasa aiwatar da ko daya saboda shi a yanzu babu abinda yafi bukata kamar samun natsuwar mumy muryarsa a ƙausashe yace "malama ki dan matsa can mumy ta samu wadataccen iskaa kin wani manne mata kina kokarin ....."
"kai ma ka matsa mana cikin ni da kai wa ya hanata shaƙar wadataccen numfashi ? ta kasheshi tana zabga masa harara " nifa bana son damuwa dan Allah kowa yayi lamarin gabansa kawai zai yi magana mumuy tayi saurin d'aga masa hannu alamun yayi shiru umarninta yabi bai sake cewa komai ba ,mommy ta numfasa sannan ta cigaba da magana a tsanake" banason jin wata magana bayan amsar tambayar da zan muku yanzu "tsakanin kai da kisna idan kun rabu zaku iya manta junanku har duniya ta nad'e"?shiru ne ya sake biyowa baya , hatra d'akin ya sake daukar shiru tamkar babu wasu halitta acikinsa kisna ta d'ago idanunta a hankali ta kalleshi dan ganin yanayinsa wani kallo ya watsa mata wanda yasa take hantar cikinta kadawa , ta tabe masa baki qirjinta ya bugawa da karfin gaske .
"ina tambayarku kun min shiru zaku iya manta junanku har abada ? Still shiru suka yi suna kallon mommy "Ni nasan bazaku iya manta junanku ba har duniya ta nade da tunanin juna zaku mutu amman idan amsarku ta kasance "eh zaku iya manta juna sai nasan abun yi ........"
Jin yadda suka yi shiru yasa ta waigo gefen da Aliyu yake da gefen da kisna take makale daita tamkar zata mata numfashi taga suna kallon juna tayi murmushi irin nasu na manya "mai yasa kuke kallon juna ku bani amsar tambayata mana kun min shiru suka sake yin shiru kowanensu na jiran yaji abinda d'an'uwansa zai furta "nasan baza ku iya amsa min wannan tambayar ba bari na faɗa muku abinda zai sa ku shiga hankalinku wallahi muddin kukayi kuskuren barin juna karshenku wahala mai tsanani ,kuma sai ta shafi rayuwar ya'yanku saboda zaku raba musu hankula , saboda kai Aliyu wata matar zaka aura kema Kisna wani mijin zaki aura kuma duk wanda zaki aura bazai kai uban ya'yanki ba ,hakazalika kai ma nawal bazata zama tamkar Kisna agurin su Aryan ba ,da zaran ta samu nata zata manta dasu ba kowace matar uba ke rike masa yaya tsakani da Allah ba ta karashe maganar tana sauke numfashi da kyar Aliyu ya sake tashi ya dauki goran ruwan da yayi wurgi dashi yaga da sauran ruwa aciki ya mika kai bakinta ta kurba tana lumshe ido "na gode muradi Allah yayiwa rayuwa albarka Allah ya yaye maka zafin zuciya ".
"gara kan kina yi kina masa addu'a, wannan zuciya kamar ta mutanen farko ,zuciya a wuya kamar kuturu ba'a jin rarrashi bare hakuri kallonta kawai yayi ya furzar da iska tare da jan tsaki ,ta watsa masa harara tana hura masa hanci dan ta sake tunzura shi ,a ranshi yace kiyi duk iskanci da kika ga dama ganin idon mumy ne zamu hadu ne .."
"Kana magana ne ? tayi maganar cikin jan hankali ."
"ke kisna ban son iskanci sa'anki ne"? tayi shiru "ki shiga hankalinki dan kice kika fara kawo zance rabuwa a tsakaninku da muradi bayan kuma kece za kiyi hakuri dashi domin kin zo gyara kuskurenki ne a gurin mutumin da yake tsananin fushi dake dan iskanci sai kina fada masa magana "kiyi hakuri mumy , "bani zaki bawa hakuri ga wanda zaki sake bawa hakuri nan kuma yanzu a gabana saboda ko babu aure a tsakanin ki dashi d'anuwanki ne bai cancanci wasu abubuwa daga gareki ba , muryarta a raunana tace "to ..to kayi hakuri ".
"haka ake bada hakuri ki hada kalamanki guri daya ki bashi hakuri ta shagwabe fuska kamar zatayi kuka tace "kayi hakuri ".. shiru yayi yaki magana dan zafin da zuciyarsa keyi ba zai bar shi ya amsa mata ba .."Kisna na kiraki da babban murya karki sake zance rabuwa tsakaninki da muradi saboda ina matukar sonku tare bana son ku rabu, rabuwarku daidai yake da shigata damuwa "Ni kuma zafin da zuciyata take akan shi fa mumy ni kadai fa nasan abinda nake ji kar a waye gari a iske bana numfa........" Da ikon Allah babu abinda zai sameki idan kika zauna dashi tsakani da Allah zaki samu lada mai dimbin yawa sannan zaki jiyar da mahaifiyarki dadin da bata bata jin irinsa ba ,zata sake magana mumy ta dakatar daita kana ta maida hankalinta kan Aliyu .....
"aliyu wacece ni agurinka "? da kyar ya iya bude bakinsa muryarsa can kasa yace "Mother " yana riko hannunta cikin nashi "tabbas ni uwarka ce shiyasa ma nafika jin haushi akan abinda kisna ta maka ,abinda tayi ya balain tsaya min a rai ya dameni ya daga min hankali saboda na fahimci halin daka shiga a lokacin amman duk da haka yana da kyau ka yafe mata a karo na biyu dan Allah ku fahimci mahaifiyarku ina son ganinku cikin farinciki dan Allah ku zauna lafiya dan kwanciyar hankalina shiru suka yi zuciyarsu na dokawa da sauri iska ya furzar yana Kallon Kisna itama shi take kallo "mai yasa mommy zata masa haka akan kisna "? "Mai yasa zata sa igiya ta daureshi akanta ? "Aliyu ta sake kiran sunansa muryarta a sanyaye kamar zata zubar da kwalla ," ka saki ranka nasan halinka kana da tsananin fushi da riko a cikin zuciyarka