Showing 489001 words to 492000 words out of 495987 words
Chapter 164 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
da jikinsa "wato ke kinsan ta kan mugunta kou ai kuwa zaki jiki wallahi "am really sorry daman gobe nake cewa zamu dawo, kinsan Allah daga nan bazaki ko'ina ba sai gida dan na gaji da zaman kadaici ni kadai a gidan kamar wani maye ko'ina yayi min shiru babu dadi ko kaɗan ,ta kwashe da dariya" to ka bari na shiga na dauko mayafi na ya kalli kan kujera inda hijab din mumy yake ya nuna mata da baki "to bari nayi wa mumy sallama "shi kuma rantsuwar da nayi fa babu yadda ta iya ta dauki hijabi din mumy ta zira shi kuma ya saba mother a kafad'ansa ya kwashi iyalinsa sai gidan suka bar mumy dasu aryan dan suma yanzu basu qaunar barinta suje wani guri ko sunje kuwa basa iya bacci sun fi so sujisu a karkashin kakannensu kamar yadda ta sabar musu ."
gida daga su sai mother hakan yake basu damar cin karensu babu babbaka dan kullum ganin junansu suke tamkar sabon ango da sabuwar amarya Allah yayi musu kyakkyawar turba, a yanzu kisna ta zama mudubin gidan muradi baya ganin kowa a gabansa sai ita bama gidan ba hatta family dinsu kowa cikin qaunarta yake daman ita ce damuwarsu , yanzu kwanciyar hankalinta ya kwantar da nasu ,
kullum cikin sa albarkar iyaye take musamman mahaifinta ji yake kamar ya bata rayuwarsa a dalilin farinciki da take bawa muradnsa mahaifin nawal ya kira muradi yafi sau babu adadi amman bai daukan kiransa nawal ta fashe masa da kuka dady "nace maka ka nemi iyayen goyonsa wallahi nasan zai maidani nifa da shi kadai zan iya rayuwa idan babu shi mutuwa zanyi tunda mahaifinta ya runtse Idanunshi bai buɗe ba yana taya diyarsa bakinciki da jimami yana matukar son nawal a rayuwarsa kasamcewar ita kadai ce lafiyayyen acikin yaransa babban dansa nakasashene komai sai an yi masa diyarsa ta biyu halima ta dade da mutuwa gurin haihuwarta ta biyu sai nawal shiyasa ya dauki dan duniya ya daura mata sam baya son damuwarta yaso ta hakura da muradi ne ta samu wani ta amman tunda ta nace babu yadda zai yi dole ya nemi alhj realwan ."
a lokacin mahaifin nawal ya nemi dady domin ayi sulhu yace babu komai komai ya wuce ta shirya dawowa d'akinta cikin satin waya kawai dady yayi wa muradi yace babu komai ya amince amman yace ya tainakesa ya fadawa kisna da kanshi dan shi bazai iya fada mata ba "kenan tsoronta kake ji ?"a'a dady bana dai son ganin bacin ranta ne to shinkenan kazo min daita yau da daddare suna gama waya ya kira afra yace tazo itama yana son ganinta ."da misalin karfe takwas suka kamo hanyar zuwa gidan dady ,kisna ta kalli muradi taga duk baya cikin farinciki ransa a hade "wai lafiya kuwa tun d'azu nake kallon yanayinka wani iri ?,babu komai ya fada yana damke hannunta cikin nashi ya ɗan waigo inda take ya sakar mata laulausan murmushi suna zuwa suka iske ya badamasi zaune yana jiran fitowar dady hannu muradi ya bashi suka gaisa cike da girmamawa haka ma kisna ta gaishe dashi suka zauna byn kmr minti biyar sai ga dady ya fito sanye da jallabiya gbdy suka hada baki gurin gaidashi ya amshi mother yana mata wasa ko cikakken minti goma dady bai yi da zama ba sai ga afra duk ta rame tsufa ma ya fara bayyana ajikinta ,nan take ta sha jinin jikinta ta durkusa har kasa ta gaishe da dady suka gaisa da kisna batare da sun gaisa da ya badamasi da muradi ba a ganinta tunda basa sonta meye amfanin gaisawa dasu ? ."
Falon ya dauki shiru can dady ya kalli afra "kenan har yanzu bakwa gaisawa da yanuwanki?shiru tayi ta kasa cewa komai numfasawa yayi kana ya kwantar da mother akan kujera a nan kusa dashi saboda bacci ya soma ɗaukarta ya kalli ya badamasi da muradi sannan ya fara magana a natse cike ban tausayi " hakuri dai da kuke ganinsa wani abu ne da yake da falala a addinin musulunci , kusan babu abinda ya kai shi falala saboda Allah subhanahu wata'ala da kansa yana cewa "
إِنَّما يُوفَّى الصَّابِرون أجْرََهُمّ بِغيْرِ حِسابٍ
Lalle masu haquri za'ayi tacika musu ladansu acikin mizanin batare da hisabi ba, duk lokacin da wani bala'i ya fado wa mutun ko kuma a kayiwa mutun wani abu mara dadi amman ya mallaki zuciyarsa yayi hakuri kuma yayi hakurin nan saboda Allah to zaayita rubuta masa lada har iyaka yadda Allah yaso shine abinda Allah subhanahu wata'ala yake nufi me hakuri kadai yake samun irin wannan ladan babu wani aiki da mutun zai yi da za'a yita bata shi lada batare da lisafawa ba ,badamasi ka duba kaga muradi bani na kawo shi duniya ba yau an wayi gari na kiransa umarni na bashi na ya maida matarsa nawal kuma kai tsaye babu ja inja babu jayayya yace min to amman Kai dana haifa yau tsawon shekaru huɗu kenan ina binka tun daka saki afra amman daidai da rana daya baka taba amsa min da zaka mayar daita shin byn laifin data maka akwai wani laifi ne ?yayi shiru yayi kasa magana " kisna ta kalli muradi da sauri fuskarta da alamar tambaya da kwayar Idanunshi yayi mata magana ta zagmasa harara tana kawar da fuskarta "ko kisna da tayi mana laifi ta 'bata mana rai ta musguna mana ta nuna mu din ba komai bane, ta wulakanta mijinta ta tozartashi yau gata a karkashin mijinta sun cigaba da rayuwa me yasa bazaka yafe mata ka dawo daita ba ?dady ya karasa maganar yana ƙoƙarin zubar da hawaye atare suka dawo gabansa gbdy suna kuka har afra "kayi hakuri dady ka daina masa maganata wallahi na dade da cire zan sake zaman aure da ya badamasi ,dady ya shiga girgiza masa kai "yana tausayinta yana tausayawa iyayenta shekarunta na tafiya duk sauran yan'uwanta suna gidan mazajensu "ni dai nafi qaunar ganinki a karkashin ikonsa idan har zai iya min wannan alfarma" zai mayar daita a gobe nan tunda haka shine farincikinka numfashi dady ya sauke sannan ya mike yana cewa kisna ta biyosa , ta shiga d'akinsa ta gansa zaune a bakin gado ta samu guri ta zauna a kasa qirjinta na luguden bugawa "kisna mijinki zai dawo da nawal sai dai yace yana gudun damuwarki to karki yarda ki nuna masa bai isa ba a gidansa, kada ki kawo masa hayaniya ko tashin hankali ki zauna lafiya da abokiyar zamanki ,idan ma bata biki ba ke ki bita ku zauna lfy ba wani abu bane duniyar ma guda nawa take nasiha sosai yayi mata mai ratsa jiki tana kuka har da shesheka ita ba dawowar nawal din ne bata so ba tashin hankali take gudu dan sam bata ga ta inda take son su zauna lafiya ba , gashi ita yanzu ta saba da rayuwa ita kadai da mijinta .."
acan falon ma muradi tashi tayi ya shiga dakin mumy ya bar afra tana kuka ,ya badamasi ya tsira mata ido yana kallonta tana kuka ",kin cire rai da zaki sake zaman aure dani saboda bakya sona ?'ta d'ago idanunta a hankali ta tsura masa sai dai ta kasa bashi amsa illa ta mike ta juya ta fice a falon yana zaune yana kallon bayanta dan dole zai maidaita ko babu darajan Iyaye shi kansa danne zuciyarsa kawai yake amman akwai soyayyarta me karfi a cikin zuciyarsa ."akan hanyarsu kisna ta komawa gida kuka kawai take muradi na rarrashinta tace" taji amman kafin nawal ta dawo ya gyara mata saman gidan ta koma yace an gama ranki shi dade duk abinda kika ce shi za'a yi ko cewa kika yi baza'a dawo da nawal ba dole ne a bi dokar uwargida sarautar mata "ka jika kamar idan nace zakayi ne ?,zan yi mana me zai hana da a min rikicin gangan gara nabi doka da oda cikin satin yasa aka gyara mata sabon bangarenta itama nawal ya gyara mata part dinta na da ranar lahadi aka tsara zaa mayar da auren nawal da muradi ya bada da afra amman sam afra taki sai na nawal da muradi aka mayar kuma a ranar ta tare da Ahmed dan yayarta sai dai ta dawo gidan ne da shirin zama na dindindin babu tashin hankali har gida mahaifin nawal yazo yayiwa dady godiya bisa karamcin da yayi masa dady yace ",babu komai ai an zama daya nawal diyata ce har abada Allah ne ya hadasu da dana dana fi so kuma take qaunarsa kaga dole ne nima na sota." Haka ne Allah ya sake haɗe kansu sai abu na gaba Ina neman wata alfarma mahaifin nawal ya fada dady ya fuskancesa ,
akan maganar aikin nawal kayiwa yaron magana domin itace ke kula da wasu daga cikin kasuwancina na kasashen duniya shiru dady yayi har sanda ya dasa aya sam baya jin muradi zai amince dan ko kisna da take gabansa a yanzu bai ji yana maganar zatayi aiki da takardunta ba bare aikin kasa da kasa ,bari dai na kirasa inji cewar dady nan take dady ya kirasa yayi masa bayanin komai shima muradin shiru yayi yana mamakin hauka irin na mutumin sai daya numfasa sannan yace "dady zamuyi magana da nawal din abinda ake ciki zata masa bayani ya tsaya sai dady ya kashe wayar tukuna yana jinsa yana yiwa mahaifin nawal bayani a hankali ya shiga part din nawal jikinsa sanye da wando jeans baki da riga dark green yayinda kafafunsa ke sanye da takalmin canvers baki haka ma kansa facing cap ne baki tana ganinsa ta soma bare baren neman gindin zama ya zauna yana dubanta ta tsiyaya masa ruwa acikin glas cup ta mika masa bai ki amsa ba, ya sha kaɗan ya mika mata "da zamuyi aure a tun farko munyi alkwari dake cewar zaki ci gaba da yawo kasashen duniya ?tayi saurin cewa a'a ,to me yasa yanzu mahaifinki yazo wa dady da batun ?gaskiya ban sani ba amman zan kirasa ,well wanan ya rage naki idan zaman aure zakiyi idan yawon kasashen duniya sai ki zabawar kanki yana gama fadar haka ya mike ya fita ta sauke naunayen ajiyar zuciya gara tayi zaman aurenta ya fiyye mata alkhairi dan babu komai acikin yawon zuwa kasa da kasa sai zubar da mutunci ka dinga cudanya cikin maza zuciya kuma bata da kashi nan take ta kira mahaifinta ta sheida masa ita zaman aure zatayi ga lawan idan ya qara tasawa ya maye gurbinta lawan dan farin yayarta halima ne yana daf da karasa karatunsa a London ."
****
Babu laifi kisna ta dan sakarwa nawal fuska, nawal na zuwa saman kisna itama tana zuwa nata sai dai ita kisna bata fiyye zuwa ba gaskiya sannu a hankali suka ci-gaba da rayuwarsu tana jan su aryan ajiki sosai a duk sanda suka zo gidan zata dinga haba haba dasu tana nuna tana bala'in son su din nan, barin ma idan akwai idanun mahaifinsu haka ne yasa muradi ya fahimci sauyawarta kuma yayi farinciki , duk kuma lokacin daya shigo da mother zata amshi yarinya tana mata wasa idan yana bangarenta tare zasu wuni itace komai nata muradi ya cigaba da daukar nauyin karatun Ahmed dan shekara bakwai yana mata fatan samun nata , tafiya tayi tafiya shekarar mother biyu kisna ta samu ciki wanda ita kusan bata so haka ba sai dai tayiwa kanta alkwarin bazata sake cire ciki ba haka zalika bazatayi planing ba zata haifi abinda Allah ya qaddaro mata dan tasan mutuwa da rayuwa duk na Allah ne , ai nawal na fahimci tana dauke da ciki nan kishinta ya motsa ta soma shan kamshi , ta daina zuwa bangaren kisna a lokacin data fi buƙatar taimakonta ko haduwa sukayi sai tana jiran kisna ta gaisheta ita kuma idan tayi yau tayi gobe sai tayi mata ba sai hakan na neman ya kawo gaba a tsakaninsu amman hakan kisna ta dauke kanta ta cigaba da tsagoginta dana mijinta dan gbdy ta gano abinda yasa ta sauya har ma akan yaranta idan sun so idan babu idanun ubansu ko kallo basu isheta ba Amman da zarar ta gansa zata fara rawar jiki ."
akwana a tashi babu wuya har cikin kisna ya kai wata shida alokacin ta dan samu lafiya ,ya fito abin sha'awa sai yayi mata mugun kyau yayinda nawal kullum idan ta kalli kisna da ciki sai zuciyarta ta motsa tayi kukan zahiri dana bani di, cikin take so ta kowani hali amman yaki zuwa wata kanwar mahaifinta ce ta samo labarin me magani haihuwa a Sudan ta hanyar wata kawarta dan haka ta sanar da mahaifiyarta nan fa suka sheidawa muradi bai hanasu ba dan shima yana son Itama tasamu nata , sun isa lafiya ta sha magani iri iri an basu wani da alkwarin tana dawowa sai ciki satinsu biyu suka dawo da takamar nan da wani lokaci zata haihu sai dai har wata uku wanda yayi daidai cikin wata tara bata samu Cikin ba ,cikin kisna ya tsufa sosai suna jiran edd dinta sai dai a daren wata laraba ta tashi ciwon nakuda daman tun magrib tana jin ciwo sai dai tunaninta ai lokacin da'aka bata bai yi ba shima gogan yana lura daita idan yaga ta cije sai yace "yaya dai baby love kodai zamu hospital ne ?sai ta yatsina fuska tace babu komai fa ta tashi da kyar ta sauko daga kan gadon ya tashi shima ya taimaka mata ta sauko yace ",ina zuwa ?fitsari zanyi ya riketa suka shi ga toilet tana tsugunawa taji kamar an sauko mata da ciwon duniya ta hau nishi nan muradi ya rikice ya fita aguje ya kira aunty ummi ya shiga ya taso nawal ta tashi Itama a rikice ta biyosa yaje ya fito da mota shida nawal suka riketa suka sata a mota duk dauriyarta sai da hawaye ya zubo mata tana salati tana cewa akira mata mumy da dady shima idanunsa ya fara cikowa da hawaye sai zabga gudu yake yana mata sannu gudu yayi sosai atare suka isa asibitin da aunty aummi ai yana gama parking ya fito sai ɗaukarta yayi dan kasa tafiyar tayi dan kafafunta sun rike sai ciki a gaba daya sauko kasa aka shiga daita labor room mintina Kadan doctor ta fito dake sun san aiki za'a yi mata suka fara shirin aiki ana aka mata shirin aiki ai ana shirin shiga dakin tiyata daita tayi wani nishi sai ga kan da karasa shiga daita akayi ta haihu da kanta likitoci kansu sun jinjina wannan girman al'amarin na Ubangiji murna kuwa agurin muradi kamar ranar aka fara haihuwa a gidansa kudi masu yawa ya dauko ya bawa nurse din data masa wannan albishir nan ya zaro waya yana fadawa mumy , madala mumy tayi a waya tana wa Allah kirari tace gata nan zuwa yace mumy shabiyu dare yayi tace" kai gafara can in samu jika kace min inyi jinkirin zuwa cikin minti talatin direba ya kawo mumy alokacin har an gyara kisna tana dakin hutu ita da kyakkyawar diyarta sannu da kokari baby love Allah yayi miki albarka abinda muradi yake fada kenan ita dai sai murmushi take ita kanta cikin tsananin murna take ta haihu da kanta "..
washegari gari aka sallameta byn an tabbatar da babu wata matsala da sassafe sai ga su aunty mufeeda ta zo tare da aunty Zahra har ma da afra kafin yamma gida ya cika makil da dangi ranar suna kowa yayi tunanin sunan mahaifiyarsa zai sa wa baby sai kawai sukaji sunan aunty ummi Aisha murna har da rafka buda tayi ,suna na kece raini akayi kuma me kayartawa kaya iri daya muradi yayi musu ita da nawal byn suna kowa ya watse aka bar aunty ummi sai da tayi sati sannan ta koma gidanta haka da rayuwa ta cigaba da tafiya cikin jin dadi da kwanciyar hankali agurin kisna ,kisna ta gina gidanta cike da ni'imar qauna soyayya da kwamciyar hankali wanda kula da junansu da kulawa da soyayya shine ya haifar musu da haka kowannensu na kokarin sauke hakin dan'uwansa tare da kyautatawa , duk abinda kisna tagani na maza muddin yayi mata kyau zata siya ma muradi tunda yanzu da kudinta wanda kasuwanci ke kawo mata ga gidan mai ga supermarket da mijin kwarai ya mallaka mata har karshen rayuwarta babu shakka mijinta kyautar Allah ne shekarar Aysha daya da rabi ta sake haihuwar namiji shima da kanta yaci sunan Aliyu suke kiransa da papi nawal ta dauki soyayarsa papi ta saka aranta komai ta samu papi ne ita kuwa kisna ido ne nata duk har cikin ranta bata son nawal din na shiga tsabgar ƴaƴanta tunda ta lura soyayyar bata Allah bace ta ganin ido ce ."
Bayan shekara shida a lokacin kisna nada ya'ya biyar aryan arif ,mother da aisha mai sunan aunty ummi papi mai sunan muradi ga wani sabon ciki ajikinta yayinda har lokacin ko batan wata nawal bata taɓa yi ba kullum dai tana kan yawon neman maganin haihuwa bata hospital bata ga na gargajiya muradi ya tabbatar mata lokacin ne ta kwantar da hankalinta muddin tana da lafiya kuma spam dinsa ke dinga ya'ya a cikin kisna itama zata haifi nata duk sanda ya fada mata haka jinsa kawai take dan gani take bai damu da rashin haihuwarta ba tunda yana da wasu ya'yan .
Ranar wata laraba aunty zee tazo duba jikin kisna dan laulayi ya fara sakata gaba suna zaune tace "ke dai kisna abun yayi miki yawa ga laulayi ga wahalar nakuda ,to ya zanyi aunty zee? qaddarata kenan Allah dai yasa muci amfanin ya'ya ameen aunty zee ta amsa ya kuwa zamanku da nawal babu wata matsala ko ?,to gaskiya dai matsalar da sauki sai dai ta iya makirci ni kuwa bana ma son na iya ,ai makirci bai yi ba a zaman aure ace sai da makirci ai mugun abu ne kowa dai ya zauna da halinsa ,ato zan zauna da halina bazan koyi halin banza ba sbd wata kishiya yanzu ko bako mukayi zai dauka nice mara kirki ni