Showing 72001 words to 75000 words out of 495987 words
Chapter 25 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
cewa" ku shigo muje wannan sarkin zuciyar ya hau sama ko wa ya kunnosa oho?.
jiki kisna a sanyaye ta shiga gidan baya idan aunty zee ke zaune hira Samir yake masa amman yayi masa banza aunty zeey tace "ranka shi dade dan allah ina son siyan wasu dogayen riguna .Aliyu bai ce mata komai ba sai gani tayi ya faka a bakin *kaafor mall* batare da yace uffan ba .
"muje kisna bani da abinda zan siya aunty " tayi magana muryarta can kasa "Ke dai muje ta bude bangaren da take ta fito suka shiga rike da hannun aryan ."
Samir yace Aliyu tun d'azu ina maka magana amman ka shareni me yasa kake takurawa rayuwarka ne kana son kisna me yasa bazaka manta komai kuyi rayuwarku ba tsaki yaja "dan Allah karka daga min hankali banason damuwa " malam ka bada kai bori ya hau kaima ka dinga shiga sawun ........
"Please Samir mai yasa har yanzu ka kasa fahimtata ne ?sanin kanka ne soyayya bata gabana ko nawal daka ga zan aura tausayi ne yasa zan aureta ba wai soyayya ba, idan kuma soyayyar zanyi kisna bata cikin jerin matan da zan iya so kayi hakuri idan maganata ta maka ciwo "
Tsaki Samir ya ja "dadina da kai wallahi taurin kai kamar mutanen farko yarinya tana sonka yanzu ka bata dama kaki " takaici ya rufewa Aliyu zuciya ya bude murfin kofa da karfi ya fito a kufule tare da saba areef a kafad'ansa Samir ya biyo bayansa yana cewa "gaskiya lamarinka akwai gyara ana gabas kana yamma kana bukatar addu'a Allah zan fadawa momy ta mike tsaye a samu ka soma soyayya "dan Allah ka rabani da batun soyayyar nan bani da lokacinta ...."
Cikin mall din suka shiga kai tsaye Aliyu yayi layin takalman yara suna tafiya suna hira da Samir har suka karaso kusa dasu aunty zee, muryarsa tasa ta jujowa idanunta ya sauka akan Samir "baby ta kira sunansa ya waigo da hannu tayi masa alamar yazo ya karaso ya tsaya a bayanta tare da daura kanshi a kafadanta "ta yani zabar kanana kaya kema kisna Ki zabi wanda kike so yayanki ya biya ,kananan kaya masu yawan gaske da dogayen riguna masu kyau ta dinga ɗauka ,duk abinda ta gani indai ya burgeta sai ta ɗauka ganin kisna ta ki ɗaukar komai ,yasa ta dinga zabar mata bom short da riguna masu kyau wanda zasu dauki hankalin mijinta sannan suka kara gaba suka bar kisna dake tsaye rike da hannun aryan kamar ance ta juya bayanta idanunta ya sauka akan mutumin d'azu yana tsaye rungume da hannuwansa duka a qirji ,tsura masa ido tayi tana kallonsa mutun kamar aljani har zata bar gurin taga gara kawai ta tsaya ta fada masa gaskiyar ita din matar aure ce ya daina binta a hankali ya karaso ya tsaya a gabanta yana kare mata Kallon tsab irin typing din matar da yake so ce ya dade yana neman irinta bai samu ba sai yau sautin muryarsa taji ta doki kunneta "tunda nake arayuwata ban taba ganin halittar data ɗauki hankali ba irinki dan Allah kibani dama na zamo abokin rayuwarki, farinciki da bakinciki ne suka hade mata a lokaci daya ,ga mijinta na tsananin nuna mata kiyayya ,ga wani na mata naci ta so shi wanda a yan sakonin da suka gabata ya daura idonsa akanta batare da yasan ko ita din wacece ba ."
Ta tsuke karamin bakinta gashi dai magana take son yi amman ta kasa sarrafa harshenta kawai ta juya zata wuce yayi saurin shan gabanta " ki tsaya ki faɗa min sunanki da address din inda kike kafin ki wuce dan bazan bari ki subuce min ba saboda na dade ina nema irinki ...."😳
Mmn sudais
[7/19, 5:32 PM] +234 803 631 5951: .💗💗💗💗💗💗
CUTAR DA KAI
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Free page 11
~TRUE LIFE STORY~
*PAID BOOK*
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
"Wannan littafin na kudi ne ,mai bukata karanta shi zai tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number alert +234 803 238 4602 domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne . "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi za'a iya tuntu'bar Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos lace da kamfala ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da chiganvy, volyal lace duk akan farashi mai sauki ,ga mai bukatar siyan ɗaya ko sari yayi magana ta wannan number 08059623096,yauwa har ma da agwalumar cotonou mai dan Karan zaki muna turawa kowani gari ...🥰🥰
A matukar harzuke ta shiga dakin zuciyarta kamar ta kama da wuta , tana k'arasa shiga cikin filin d'akin idanunta ya sauka akanshi tsaye a tsakiyar d'akin ya zuba hannunwansa duka a cikin aljihun wandonsa yayinda idanunshi ke runtse yana ciza gefen lip's dinsa na kasa a hankali , duk da bai bude idanunsa ba yasan itace ta shigo dakin duba ga yanayin da yaji bugun zuciyarsa ya qaru."
kallon second biyu tayi masa ta ɗauke idanunta akan shi ta k'arasa da sauri ta bude wardrobe ta dauko akwatin kayanta data zo dashi kasar ta ajiye akan gado ta bude ta soma dibo kayanta ɗaya bayan ɗaya tana zuba aciki ,still bai bude idanunshi ya kalleta ba bare ya dakatar daita daga abinda take ƙoƙarin yi ya cigaba da ciza lip's dinsa , hakan yasa taji sabon ɓacin rai ya mamaye zuciyarta taji muddin bata bar masa gidan a lokacin ba zata iya mutuwa.."
Aunty zee ta shigo dakin cikin tsananin tashin hankali ta k'arasa gareta ta rike hannuta batare da ta kalli inda Aliyu ke tsaye ba hankalinta a matukar tashe ta soma magana "mai kike ƙoƙarin yin saboda Allah ? "Kiyi hakuri mana
duk fa abun bai kai haka ba, idan fa rai ya ɓaci hankali baya bata kisna , ki dawo hankali ki natsu dan girman Allah Karki yi abinda zai janyo bacin rai fiyye da wanda muke ciki yanzu ".Tun da aunty zee ta soma magana kisan bata furta komai ba ta cigaba da zuba kayanta cikin akwati zuciyar na wani irin zafi da ciwo , haka shima Aliyu bai ce komai ba sai sake juya musu bayansa yayi yana furzar da iska mai tattare da bakin ciki ".
Kisna na shirya kaya aunty zee na dauka tana maida wa cikin wordrobe tana bata hakuri , wani sabon kuka ne ya kufce mata , hawaye sai turereniyar zubowa suke daga cikin kwarnin idanunta "mai kike son nayi aunty zee shine fa da kanshi yace na bar masa gida "? Tayi maganar cikin tsananin kuka wanda da kyar muryarta ta fito "nasani amman dan girman Allah kiyi hakuri ko zaki tafi ba yanzu ba saboda tashin hankalin da mommy zata shiga Sam Sam mommy ba zataji dadi faruwar haka ba. tayi maganar tare da juyowa ta kalli inda Aliyu ke tsaye har lokacin tamkar babu wani halitta dake motsi agurin, ya aliyu ka bata hakuri dan Allah sannan ka dakatar daita dan gaskiya kayi kuskure abinda kayi sam bai dace ". Bazan yayi daita qirjinshi na wani irin dokawa da karfin gaske "saboda me zai bata hakuri bayan bai ga abinda yayi mata ba ,idan zata zauna ta zauna idan zata tafi ta dade shi dai bazai wani dakatar daita ba yayi maganar aransa yana furzar da iska mai zafi ....
kisna ta sake rushewa da wani sabon kuka mai matukar cin rai ganin ko kallonsu Aliyu bai yi ba bare ya kula aunty zee dake masa magana ,ta d'aura kanta a kafad'arta aunty zee numfashinta na barazanar daukewa saboda kukan da yaci karfinta "kisna !kisna!! Aunty zee ta ta kira sunanta a rude tare da rungumeta a jikinta suka zauna a bakin gado tana cigaba da kiran sunanta , da kyar kisna ta janyo numfashi ta sauke zuciyar na mata wani irin azababben zafi da ciwo , aunty zee ta mike ta tsiyaya mata ruwa a glass cup ta mika mata "ki sha ruwa kisna ko zaki ji sanyi babu mutsu kisna ta amsa cup din ta kai bakinta ta kurbi kadan ta mikawa aunty zee sauran ,aunty zee ta amsa ta ajiye ta cigaba da bata baki .
cikin haka aryan ya shigo dakin yana kuka aliyu ya juyo a hankali yayi taku daya yana ƙoƙarin kamoshi zuwa garesa , amman tuni yaron ya karasa gurin uwarsa dake kuka tamkar ranta zai bar gangar jikinta , ya haura saman gadon ya rungumeta ta baya yana furta mata kalmar "sori mommy , papa ne ya saki kuka kou ?" Ki yi shiru Ki daina kuka zan rama miki kinji ".
kukanta ne ya qara akan wanda take tabbas ya'ya rahma ta juyo ta rungumeshi ajikinsa tana sheshekan kuka tamkar ranta zai fita,hawaye tausayinsu ne ya shiga gangarowa aunty zee Aryan ya soma ƙoƙarin raba jikinsa dana kisna ",mumy bari naje na rama miki "a hankali ta shiga girgiza masa kai tana kuka gumi na tsatsafo mata ta ko'ina ajikinka matse aryan tayi gam saboda kokarin fixgewa da yake kokarin yi ajikinta yadda take kuka haka arayan da aunty zee ke kuka gaba-daya an rasa wanda zai rarashi wani ."
Sautin kukansu ne ya soma damun Aliyu a natse ya fita daga d'akin yana jan dogon tsaki ya shiga d'akin da areef yake kwance ya zauna a gefensa tare da tsura masa idanunshi yana kallonsa, ganin yadda numafashinsa ke sauka a hankali yasa shi sauke numfashi da ajiyar zuciya a tare ya d'aura hannunsa akan sumar yaron yana shafawa a hankali yana jin wani irin sanyi mara misaltuwa a zuciyarsa , dan da wani abu ya samu d'ansa da sai yayi distroye rayuwarta ,sai yayi mata abinda har ta koma ga Allah bazata mantawa dashi ba taimakonta daya d'ansa yana numfashi kuma ko yanzu bazai barta ba har sai yaga mikewar d'ansa tukunan zai saurara mata ..."
"Idan kika ji ancewa mutun yayi hakuri bisa wani abu daya faru to an cucesa ne ,ki qara hakuri kisna idan kika bar gidan Aliyu da sunan yaji ko rabuwa dashi ina zaki "?"kin san dai baki da inda zaki sannan baki da masauki a gidan dady idan kin manta abinda dady yace bari na tuna miki "cewa yayi matukar ba ziyarar arziki ce zata kowaki gidansa ba baya son ganinki da suna matsala dan baki a masauki a gidansa, kuma duk ranar da kika kashe aurenki da Aliyu sai dai ki nemi wani uban amman ba shi ba, zan rokeki da ki kara hakuri kisna ki zauna a d'akinki kada ki ɗauki maganar Aliyu da mahimmcin da zai sa ki bar gidan nan ". wani sabon kuka ta rushe mata dashi tare da zubewa kasa bisa gwiwowinta ta kamkame Aryan dake rungume ajikinta "shikenan haka zan kare rayuwata cikin kunci da maseefa da tashin hankali "? "mai yasa dady da mommy suka kasa fahimtata akan ya Aliyu "?
"Mai yasa suka fi son shi akan ni da suka yi silar zuwana duniya "?
aunty zee ta mike tsaye cikin tsananin tashin hankali ta amshi aryan a hannunta sannan kamota ta zaunar daita tace " wannan soyayya daga Allah ce kisna da kuma kyautatawar da yayi musu, kin sani na sani kowa ma ya sani a cikin yan'uwa Aliyu mutumin kirki ne ,ni yanzu babu abinda zan ce miki daya wuce kiyi hakuri sannan kiyi ƙoƙarin ki adana damuwarki kafin mommy ta dawo gidan nan ta fahimci wani abu , sannan waɗan nan kayan suma ki karasa maidasu cikin wardrobe zanje muyi magana da ya Aliyu ta k'arasa maganar tana fita daga."
kai tsaye parlou'n kasa ta zarce domin yin magana da Aliyu sai dai bata samesa anan ba sai nasir da Samir da Safiyya ta samu zaune shiru tamkar waɗan da aka turo musu da sakon mutuwa , ta Kallesu daya bayan daya sannan tace "ina ya Aliyu ko ya fita ne "?Safiyya da nasir ne suka hada baki gurin ta bata amsa da bai sauko ba yana sama ,
yayinda har lokacin samir ya kasa furta komai sannan ya kasa aiwatar da komai dan jin zuciyarsa yake kamar zata kama da wuta yau da wani ne ba Aliyu ba yayiwa kisna irin wannan wulakanci Allah ne kadai zai rabusu amman akan Aliyu babu abinda zai iya yi ko dady yaji yayi magana akan lamarin sai ya bata masa rai bare matsayin Aliyu ya zarta komai a zuciyarsa ..."
Har aunty zee ta juya zata koma sama ta tsaya batare data juyo ba tace "dan Allah abban Junior ka dawo daidai kar mommy ta dawo ta fahimci wani abu ,wannan matsalar tsakaninsu ne kuma inshallahu komai zai dawo normal yanzu batare da bata lokaci ba , tsakanin miji da mata sai Allah ko mutun ya shiga faɗansu kunya zai ji tayi masa hannunka mai sanda saboda lura da tayi gaba-daya yanayinsa ya sauya tana gama fadar haka ta hau sama da sauri ta shiga dakin mommy ,nan ta samesa zaune ya tasa areef gaba yana kallonsa hawaye na tsiyayo wa daga idanunshi jin motsin shigowar mutun yasa yayi saurin ɗauke hawayensa da hannunsa , sai dai ya makaro dan ta rigada ta gani .
girgiza kai aunty zee tayi sannan ta samu guri ta zauna akan kujera tana kallonsa sai data numfasa sannan ta kira sunansa a natse " ya Aliyu .... Bai amsa mata ba haka zalika bai waigo inda take ba ,sanin datayi yana sauraranta yasa ta cigaba da magana "dan Allah ya Aliyu ka canza ,a zahirin gaskiya ban ji dadin abinda kayi wa kisna ba , kuma nasan ko mommy tana nan kai zata bawa rashin gaskiya akan abinda ya faru "."ina dalilina nayi haka , barinta gidan nan shine abinda zuciyata ta yanke akanta idan taga zata iya ta cigaba da zama a gidan idan bazata iya ba ga hanya nan dan Allah Karki sake bata hakuri akan lallai sai ta zauna ki bari ta wuce duk inda zata dan nima nafi bukatar haka "."Uhmmm Aliyu ka kuwa masan abinda kake faɗa kama ajiye batun aurattayar dake tsakaninku kai da kisna yan'uwa ne na na jini kasawa ranka kisna Aliyu suna tare muddin rai mutuwa ce kawai zata rabasu "stop saying that zainab I don't like what you are doing Ina nugun ganin girma da mutuncinki saboda ke din mai mutunci ce kowa ya sani ...... ".
"bazan daina fadar haka ba ya aliyu saboda bayan jinin na y'an'uwanta akwai wani jini na musamman dake gauraye acikin jininku ko kaki ko kaso kisna da Aliyu abu guda ne "dan Allah ki daina faɗar haka kina maseefar taba min rai wallahi "",Babu wani ɓacin rai hakuri ma ya kamata kaje ka bata saboda kayi mata ba dade ba . "wannan maganar ma ba mai yiwa ba ne dan Allah ki daina fadar haka banaso ina ganin girmanki zainab saboda me zan bata hakuri "? "Laifin mai nayi da zan bada wani hakuri "? yayi mata tambayar ajere ransa na sake ɓaci sannan ya cigaba da magana cikin zafin zuciya "bana tunanin abinda nayi ya sa'bawa Shari'a to saboda me kike tunanin zan bata hakuri "? yayi maganar yana rike hannun areef yana jin yadda hannunsa yayi sanyi "yanzu kana son fahimtar dani cewar ba kayi kuskure ba Kenan "?"Yes of course ban yi komai ba wallahi ,kin kasa dai fahimtata ne kawai saboda kina ganin kamar nayi kuskure alhalin ni Kuma nasan babu kuskure dana akan za'a kashe min da.... .....".....
yayi shiru ya kasa karasa maganarsa yana kallon kofar d'akin ,itama aunty zee kofar tabi da kallo ganin kisna ta gani tsaye idanunta na tsiyayar da ruwan hawaye muryarta cikin kuka tace "ki yarda aunty zee bai yi min laifin komai ba ,ni kuma daman na ɗauki laifina ya dai kasa min uzuri ne amman nasan nice da laifi wallahi tunda nasan halinsu aryan basa zama guri daya ". ta runtse idanunta wasu hawaye masu zafi da ciwo suka sake gangaro mata .
"ni kaina a yanzu zanso rabuwa dashi
sai dai bazan iya kallon idanunshi nace na tsaneshi ko nace bana bukatar rayuwata dashi ba saboda darajan ya'yana, bazan iya kallon idanun uban ya'yana nace banason shi bana bukatarsa arayuwata ko bana bukatar had'uwa dashi a lahira ba kamar yadda ya fada min ".
A matukar fusace yace "kinji ba kinji abinda wannan wawiyar take cewa ko zainab wato ma darajan ƴaƴanta takewa komai ? "ai daman nasan abinda ke zuciyarki kenan shi yasa nake son rabaki da su gaba-daya na canza musu wa.........."tayi saurin katse masa hanzari ta hanyar cewa " duk abinda zaka faɗa ya Aliyu ka fada amman bazaka taba canzani agurinsu arayan ba saboda nice nan na dauki cikinsu na tsawon wata tara da kwanaki kuma nayi na kudarsu ...." Ni yanzu Abinda zaka min tunda baka bukatar zamana da kai ka taimaka ka wankeni agurin mahaifina tunda nayi iyakar ƙoƙarina naga mun sasantar kanmu muyi zaman lafiya da juna amman kaki ," ba dai baka son zama da kisna ba ? yayi shiru tare da jan tsaki "to ka taimakawa rayuwata ka wankeni agurin iyayena kafin ka sawakemin aurenka dake kaina wallahil azim ina bukatar takardar saki daga gareka ,ka sake ni ka huta rayuwarka nima na huta " .
tunda ta fara magana ya dauke kanshi akanta sai dai jin maganarta ta karshe yasa Ya d'agowa idanunshi a hankali yayi mata wani kallon banza sannan ya ɗauke kanshi ya cigaba da kallon areef zuciyarsa na masa wani irin tuttukin bakincikin, sosai aunty zee ta tausayawa halin da kisna take ciki gashi dai a shirye take data sadaukar masa da rayuwarta amman ya kasa fahimtar kisnar da data yanzu akwai bambamci "ya Aliyu karka biyewa zuciyarka kayi hakuri dan Allah, karka biyewa maganar kisna tana cikin