Showing 372001 words to 375000 words out of 495987 words

Chapter 125 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt

gidan   suka   iske  mutane  suna  zaman   jiran  karasowarsu  shiru tayi tsaye tana kallonsu daya bayan daya zuciyarta  na  bugawa   granny  ta kamota  tana kokarin   zaunar daita  dan  jikinta babu  kwari  ta  zauna cike da  ɗari dari zuciyarta  na cigaba da bugawar  da yake  da matsanancin karfin gaske ."

  Falon   shiru  har lokacin babu wanda  yayi  kwakwaran  motsi yayinda   idanun   dady  dana mumy har ma dana sauran mutanen dake zaune a falon  suke    kanta  tare  da rafka  tagumi  itama cikin tsananin faduwar gaba take   cigaba  da kallonsu,  byn   kamar   minti shabiyar "dady  yayi gyaran murya ya  fara magana a tsanake   "sakina  me  yasa  kika iya cin amana  da yaudara da ha'incin  da cazawa mutane  zukata ?  " yayi  mata  tambayar a jere  yana kallon  cikin  kwayar idanunta da suka jeme sukayo waje  "kullum  zuciyarki   na  sake  bushewa babu digon  imani   acikinta  idan har  baki yarda Allah daya bane  sai yaushe kisna ?"  lokaci  yayi daya kamata ki  buɗe  dodaddiyar kwakwaluwarki  ki san  abinda  duniya take ciki , kina  nunawa   mutumin da  bai  ji  ba  bai gani ba kiyayya mara dalili   wanda  har kiyayarsa  tasa  kika kashe  masa ya'ya har  uku a  rana  daya  sai kuma  ga  wani  sakkayar   Allah  ya  sake nuna   ishararsa  akanki ya   nuna  karfin  iko da mulkinsa  akanki  kika sake  ɗaukar  cikinsa na wata  hudu da sati  daya a karo na biyu  ,me  zaki cewa  Allah  akan wannan ? " akan  kujera  take  amman  bata san  lokacin data  zubo  kasa  bisa  gwiwowinta  tare da  dafe  qirjinta da duka hannuwanta  tana zaro ido tare da  girgiza  kai sannan ta  bude  baki  da kyar  muryarta na rawa  "wa wai dady   ni  ke dauke da ciki  har  na  wata  hudu da sati daya ? ya gyada mata kai alamun" eh"" kenan cikin na  nan  bai fita ba ?

"Inna  lillahi wa Inna ilaihi raji'un  gbdy  Jamar  dake zaune  a gurin suka hada  baki   gurin furta hakan  , wannan   kalmar  da  suka furta   yasa  ta  fahimci  lallai  ta  gama  tonawa kanta  asiri a fili tayi maganar  "kenan shima wannan  cikin kinyi kokarin  zubarwa ? sautin muryar mumy ta karad'e  falon cikin tashin hankali "kisna  tayi  shiru  tana  zazzare idanu   qirjinta   na  faduwa   "lallai    kisna baki  da  imani sam zuciyar  kafirai  ne  dake    inji  cewar  mumy     wacce  ta  mike a zuciye  ta hau  zuba ma kisna  maruka "walllahi  da kinyi  gangancin  cire cikin nan  da ni da  kaina  zan  kasheki  mara imani  kawai  babu  wanda bai tofa  albarkacin  bakinsa  ba  haka babu wanda bai  yi  Allah wadai daita ba "maganar   daurin  auren babu " inji  cewar alhj  Nuhu  wanda ya kasance yaya ga alhji realwan  alhji marwan yace  "babu  mana yaya  tunda   babu   yadda  za'a  daura  mata  aure da ciki sai  ta haihu zan nemi yaron  idan yana sonta ya  jira har  ta haifa mana  abinda  ke  cikinta  sai suyi  aure wata irin zufa ce ta   shiga   karyo  mata  ta  ko'ina a sansar jikinta tamkar wacce akayi wanka da ruwa   dan   kuka   ma  kasa  yi  tayi  ta   dawo  tamkar   gunki  a durkushe  "daga yau  ta dawo gidan nan kenan  da zama har ta haihu  dan zamanta agurina  bazan  samu natsuwa  ba  inji cewar granny  ban da ma mugun  hali irin na  kisna kinsan  kina da ciki zakiyi aure da ciki saboda Allah "ba  jahilci da haukan kiyayyar  na damunta ba  ai dole tayi ai  nan dai suka yita tautaunawa akan batun  cikin ."

kusan  kisna   ta  daina   fahimtar  abinda suke  fada har   sai data dawo  dakinta    sannan  tunaninta  ya dawo jikinta  ta  tashi ta zauna tare da   daura hannuwanta duka  akanta  tana  tunanin  maganganun 'yan'uwanta tana  kokarin tantace gaskiya daga karya kawai  taji zuciyarta ta yarda cikin da tayi kokarin zubarwa na nan bai girgiza ba    babu  wani karya a ciki maganar su , toshewar baseera ce kawai irin nata   ta kasa fahimtar cewar cikin bai   fita ba yana nan   tunda tun dan jinin da ta gani bata sake gani ba  aiko  ta  rusa    kuka da kururuwa  tamkar  wacce  uwarta da  ubanta suka mutu "wannan  cikin gaskiya ne  amman   duk  halin da zan ciresa  sai  na ciresa   ko sama da kasa zasu haɗe bazan haifi  cikin  nan ba wallahi bazan yi hakuri zaman  gidan nan ba wallahi  , bazan zauna ba gbdy na gaji  na gaji da zaman gidan nan  duk   ta burkice acikin dakin  tana sambatu  zuciyarta  ba bugawa da karfi , haka ne yasa kafin gari ya  waye jinita ya hau ta sume  da   kyar aka samu ta  dawo haiyacinta babu wanda  ya  tsaya rarrashinta  tunda kowa yasan yadda zuciyarta take da kafiyar tsiya  sanda ake rarrashinta  da ban hakuri lokacin zuciyarta   ke sake hautsinewa   tun daga lokacin kacokam  'yan gidan suka maida hankalinsu  gareta suna bata  kulawa bata  cass bare  ass  sai  a  girka akawo  mata  amman yadda  aka kawo mata haka za'a dauke bata ci a tunaninta  yunwa  zai sa cikin  ya wahala ya zube".

******
Bangaren  musa  kuwa   sanda yaji  tabbas  cikin muradi ne ajikinta   ciki tashin  hankali da  rudewa  ya zube kasa  daga tsaye   yana furta "kisna ta cucesa  ta yaudaresa  taci amanarsa  gbdy mahaifiyarsa ta rasa gane  kansa da gindinsa  ɗan sai zuba sambatu  yake  wani irin kuka da qara yake yi mai ban tausayi  kamkameshi mahaifiyarsa tayi tana fashewa da kuka domin tasan  dole zai ji abun a zuciyarsa  a yadda ya kwallafa rai akanta  zuciya  sai tafasa yake jikinsa yayi zafi  sai kuka yake yana kiran  sunan  kisna  ta cucesa  har   sai   daya  kai  ga  kwanciyar  a asibiti  laida ruwa  biyar  ya  sha  sannan ya  dan dawo  daidai sai dai har lokacin zuciyarsa na cikin  kuncin  abinda kisna tayi masa dan idan wani ne ya fada masa zata iya bawa wani namiji kanta bashi ba  zai mutsa  sai  ga sheida wacce babu karya sai zallar gaskiya tunda ba'a shan ciki a ruwa yayi bakinciki sosai  da wannan cikin gidansu cike da mutane ana jajantawa mahaifiyarsa abinda ya faru shi kuwa musa duk abinda suke hankalinsa baya jikinsa kallon kowa kawai yake  ..."

Yadda  musa ya daga hankalinsa haka kisna   ta  daga  hankalinta  aunty ummi  ta  kalleta   tace" kina ta  faman  kuka  da kin cin abinci ko mutuwa aka  miki  sai  haka "ai dama  mutuwar nayi wallahi  na huta da wannan  bakinciki Allah ya sani  ni  bana son cikin nan yadda bana kaunar wanda yayi  cikin haka cikin bana son shi  mufeeda ta kalleta cikin jin haushi maganarta  tace " to kada Allah yasa ki soshi din  ai tunda Allah  nason shi  sai  kin haifeshi da izininsa muguwa   kawai  mai muguwar zuciya  ta Allah ba taki ba  wallahi koda  wasa  wani  abu  ya samu cikin nan  sai  munyi  Shari'a dake "  zahra ta  karɓe maganar"wallahi ki ma shiga hankalinki  tun wuri dan akan wannan cikin zaki jawowa kanki matsala da kowa a gidan nan   dan zaki karawa kanki sabon tsana ne kawai  , idan kika hakura kika kwantar  da  hankalinki  ke kanki zaki yi mamaki  yadda  zaki  samu farinciki  maganar bakya son Wanda yayi cikin shima ai baya sonki dole tasa ya amshi aurenki, yanzu haka ma ya manta dake  a rayuwarsa dan ko sunanki  baya qaunar ji "to  yazo ya kashe ni mana tunda baya qaunar yaji sunana mugu kawai Allah ya isa cutar da yayi min  "yadda  bazaki  iya kashesa ba  haka shima bazai kasheki ba kuma kika sake zaginsa sai kin gwamaci baki da wayo   a tare suka bar  dakin  zuwa falo suna huci suka zauna har aunty ummi zata zauna ta fasa ta koma dakin da kisna take "bani wayarki "ki bar min wayata aunty ummi  "a'a bazan bar miki ba jikina na bani za'a iya kulla makirci daita tana kuka ta rike wayar gam hannu aunty ummi ta  Kamo   hannunta ta bude  da iyakacin karfinta ta amshe wayar ta sake ficewa ."

yau  tsawon kwana uku kenan mumy tana neman  layin  muradi da samir bata  samu  ba  domin fada musu abun farincikin daya  samesu  yanzu ma da take zaune a falonta  layinsa take  kokarin  kira    cikin  tsananin  farinciki  ai kuwa taci sa'ar number ta shiga yana dauka ya gaisheta cike da girmama wa bata amsa masa gaisuwarsa ba tace  "kana  jina  muradi "...take  dady  daya  shigo   falon  ya  kwace  wayar a hannunta tun  kafin  ta ida maganarta yace "  yarona kana jina ?"  ykk ya ayyukan fatan dai  kuna  cikin koshin lafiya ? "mumynka ta dan tashi  yanzu amman dai tana lafiya  okay to shikenan ya katse  kiran ya fuskanci gabadayansu har su aunty ummi da yanzu kullum suna gidan tunda abun ya faru   "banason  muradi yasan  komai akan  labarin  cikin nan dan  zai iya  d'aga  hankalinsa  bayan  da kyar aka samu zuciyarsa ta samu natsuwa , abarsa ya huta ko  samir  banason ya sani" har kusan sati biyu  kisna  bata warware ba  tana  kwance  a daki tana aikin  kuka ta rasa wanda zata zanta da matsalar data sake kunno kai rayuwarta  a karshe  ta  tashi  ta shiga dakin  mumy ta  dauki wayarta ta  kira zee tana kuka ta fada mata abinda ya faru abun mamaki da takaici sai jitayi ta  hau kyakyale mata  dariya  domin  taji dadi  ,cikin  muryar kuka  tace "shikenan aunty zee tunda dariya matsalata ta  baki" Ni kisna  na zama abar tausayi  ni ba marainiya ba  ina fama da maraici ta kowani  bangare  babu  farinciki  "bazaki  gane bane  kisna wallahi dadi naji sosai kuma wannan shine soyayyar da muke miki  duk  wani mai kaunarki  zai so ki haifawa   ya Aliyu ya'ya Kinga  wannan cikin wallahi  wata rana  zakiyi alfahari  da abinda  ke cikinki , Allah yasa su zamo 'yan uku irin na wancan karon "ba ameen ba  Allah ya  isa  abinda yayi  min mutun kamar akuya  daga  yi  daya sai ciki  ".  aunty zee ta sake yin dariya  tace  "namijin kenan ai kuwa yau ba sai gobe ba  zan masa albashi "wallahi  kar kiyi masa  dan  wannan cikin ma rariya zai bi kamar wancan bata  tsaya  taji  abinda aunty zee  zatace ba ta katse kiran  ta soma neman  layin musa kira uku  tayi masa bai dauka ba a karo na hudu ne  ya dauka yana jin muryarta ya kashe dan shi tuni ya fara dawowa daga rakiyarta  ,tarraya  daita babu alkhairi sannan babu  abinda yake janyo masa sai tashin hankali da bala'i iri iri kullum shikenan cikin tashin hankali da guje guje uws uba yaudararsa datayi na kin fada masa gaskiyar ta bawa muradi kanta tayi shiru tana mamaki ta sake kira amman wayar na ringing yaki dauka a karshe ma ya kashe wayar gabadaya jikinta yayi sanyi tare da daukar zafi  
ta goge number dan kar mumy tazo ta gani tabi number  zata kira layin aunty afra  kenan mumy ta shigo dakin   tace "bani wayata kar na sake ganin kin daukar min  waya ta mika mata ta fice daga dakin zuciyarta na ta  fasa  mumy  ta  duba dialled  bata ga  sunan kowa ba sai na zee ta sauke numfashi da ajiyar zuciya a tare   tana kokarin  ajiye wayar kira ya shigo  sunan zee ta gani har zata kira kisna ta bata wayar sai  ta dauka daga can bangare  aka  fara magana "kina jina kisna dan  girman Allah karki taba lafiyar cikin nan zan fadawa  muradi nasan zai yi farinciki "karki fada masa  sautin Muryar mumy ya doki kunnen zee "mumy Ina yini ?"lafiya kin dai ji abinda nace  "to shikenan mumy amman ki kara sanya idanu akan kisna dan tace zata zubar da cikin  "inshallahu  ina wannan sarkin kukan  yake ?"yana nan lafiya mumy yanzu ya gama kukan nashi na gado yayi bacci sai da suka dauki minti shabiyar  suna  hira sannan sukayi sallama ".

Da  daddare  muradi na zaune  shi  da Samir  suna  cin  abinci zee  tayi murmushi  tana cewa "ya Aliyu  ka gama cin abinci akwai abinda zan fada maka  "  ya d'ago yana kallonta  yana cin abinci "uhmm  ina jinki menene shi  ?"no ka gama tukunan  a hankali ya cigaba  da cin abinci  har ya  kammala ya sake tsura mata ido "uhmm ina  jinki  zee ".kisna na......."
saurin d'aga mata hannu yayi tare da haɗe fuska tamkar wanda aka aikowa da sakon mutuwa   "banason damuwa zee sannan  ban yi  tunanin akwai wata  rana da zaki dawo min da wannan sunan ba  "ka tsaya kaji ko akan me zanyi maganar " bana  bukatar komai daya danganceta kinga ni na  wuce gurin  nawal yanzu haka  tana can tana jirana  "ni wallahi banason nawal din nan  mai siffa kaguwa "fada min dalilinki na kinta bayan ba soyayya muke ba ?"  karki manta  yadda ta taimakawa  dan'uwanki  ya dawo rayuwa kamar ta sauran mutane " . ta karya da kai tana dubansa  sannan tace "na sani but  ita ai  da alamun sonka take "kin cika shirme zee haka ake soyayya ?" ya karasa maganar tare  da  ficewa   daga falon ta maida  idanunta kan Samir  "abinda zan fada masa  mai  mahimmanci ne  fa amman kalli yadda ya watsa min kasa a ido "to yace baya so  ko dole ne ?" to kai bari na fada maka  Allah nasan har albishir sai ka bata ni " nima banason ji dan haka ki kama kanki sosai ya karasa maganar a zuciye  shiru  tayi  har sanda shima ya mike ya nufi d'akinsa ta zaro ido waje sakamakon tuno   abinda mumy ta fada mata Allah ma ya taimaketa da  basu saueareta ba da me kenan tayi ?"

*******

Da misalin  karfe  hudu na yamma muradi  na  kwance a bangarensa a gidan  da dady a gina musu a unguwar  rehab  wayarsa  tayi qara alamar shigowar sako  ya dan mirgina ya  kai hannunsa ya dauki wayar yana duba screen din wayar   ganin sunan nawal dauke da sako  yasashi   mikewa  ya zauna rigingine ya fara karanta sakon hankin kwance .

_"ya kai mai rike da zuciyata  bazan iya tsayawa  gabanka da bukatar da bansan  yadda  amsar   zata  zo min ba,  haka  nan bazan iya cigaba da rike abun acikin zuciyata  ba , Aliyu muradi  sonka nake  ,qaunarka nake, na tabbatar da haka ne tun a lokacin da ban tsamaci zan hadu da kai ba,yanzu   kuma dana zo na hadu da kai muka shaku sai soyayyar ta qara fiyye da lokutan baya , a  lokaci na dauka burgeni kake daga baya na fahimci zallar qauna ce , "gbdy a halin yanzu na nemi zuciyata a fadin qirjina na rasa  ,zuciyata babu namijin data kamu kuma ta yarda ko mafarkin qauna sai kai , zuciyata na dauke da qaunarka da alkwarin zata tsaya tare da kai a kowani hali, zata sadaukar maka da komai nata muradi kai ne ka mallaki zuciya nawal  ba zabi nake baka ba  shawara nake baka ka soni da gaskiya  hakika zakaji dadin zama dani, bazan damu da ko mata nawa gareka ba muddin zan kasance a karkashin ikonka zanyi farinciki  da wannan alfarmar zuciyata  ta makalewa sonka muradi irin son da bazai sa ta kasa fahimtarka  ba , kota sabawa umarninka  ,ko yi maka karya, zuciyata   bazata saba alkwarin data ɗauka ba sannan bazata taba son waninka ba dan ban fara sonka dan na daina ba ,  ban taba son wani namiji yadda nake sonka ba akanka  nasan soyayya gaskiya ce ba irin ta  yaudarata da maza uku suka min ba  kamar yadda na sheida maka abinda bani da  tabbacin  akai  shine ingantacciyar rayuwa a yayinda na kasa samun amincewarka mai kake jira norr  da wannan ceton ran  ka ceci  zuciyata ka soni muradi na tabbatar bazakayi nadama ba ,ka soma daukata  a matsayin masoyiya kuma wacce zata zamo uwa  ga ƴaƴanka_

Ya dade yana karanta text dinta yana sauke numfashi da ajiyar zuciya , sai  daya  baya jin  zai yarda ya fada motar  sonta  ,  kusan kwana biyu  suna haduwa daita  agurin shakatawa da  yamma  kamar yadda suka saba haduwa duk karshen sati , sun dade suna  hira sai  dai ko da wasa bai nuna mata yaga sakonta ba  dan  shi a tsarinsa baya son mace mai iya fallasa abinda ke zuciyarta barin ma a  bangaren soyayya, dan  kwantawa nawal ta kwanta masa illar dai hanzarin fito da maitarta fili da tayi.
  Ranar asabar da yamma suna zaune nawal ta tsura masa  idanu  tana kallonsa duk burin wata diya mace  muradi ya cika a dan muamular da sukayi ta fahimci mutun ne shi  mai kirki , hakuri  ,addini  ,gaskiya ga ilimin Arabic dana boko sannan kuma kyau  gashi  d'anuwanta  mai arziki mai  daukaka  wanda  duniya tasan dashi , ya  dan  bata tahirinsa  sai dai abu guda ya tsaya mata arai  inda yace mata yana da  mata a hankali ta dinga jansa da hira  kamar koda yaushe kasancewarsa mara son magana har  ta sanyo maganar soyayyarta  kamar zatayi kuka "ko matarka bazata iya zama dani bane ?"yayi mata shiru kawai yana kallonta " wallahi  bazan bata matsala ba , zan  bita yadda kake so ta karasa maganar tana riko tafin hannunsa cikin nashi tana murzawa  take jikinsa  yayi  sanyi  sai dai bai ji komai akanta ba "wallahi ko mata uku gareka ba daya ba  zan iya zama dasu, zanyiwa mahaifiyarka bibbiya ,
zan kular maka da yanuwanka ta karasa maganar tana kokarin zubar da kwalla naunauyen ajiyar zuciya ya sauke muryarsa a sanyaye yace "kada ki bari hawayen nan su zo "tayi saurin goge su da bayan hannunta tana sauke numfashi , idanunta akanshi "wasa nake miki dana fada miki inada mata,sai dai  a zahirin gaskiya na taba  aure  wanda ya kasance na zumunci ne har ma nayi missing  triple sai dai mun rabu daita " wani sanyin dadi ne ya mamaye zuciyar nawal ta sake riƙe hannunsa gam tana murzawa "ka amince min muradi "na amince miki sai dai da sharadin idan na aureki zaki zauna tare da mahaifiyata na tsawon wata shida har sai naga yanayin zamanki da mahaifiyata saboda rayuwar waje data gida akwai banbanci , bana wasa da mahaifiyata da yanuwana zasu soki dan suna son duk wani abinda nake so ".kenan kana sona ?ta fada tana bayyana tsantsar farincikinta ya dage mata girarsa daya yana ciza lip's dinsa "zan zauna tare

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login