Showing 291001 words to 294000 words out of 495987 words
Chapter 98 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
yana tunani sai ga mumy ta shigo sam bai ji motsin shigowarta ba sai jin hannunta yayi a saman gishinsa "kayi hakuri Aliyu nasan aure irin wannan da zakayi da ciwo " a firgice ya ta shi ya zauna yana kallon mumy zata cigaba da magana yayi saurin cewa "ki daina damun kanki mumy sau nawa zance miki ina son wannan auren ina wa kisna son da ban taba zaton zanyiwa wata diya mace a rayuwata ba ta numfasa tace "amman ni ina tsoron abubuwan kisna ne bana son ta cutar min da kai "karki damu babu abinda zai faru sai alkhairi a yadda nake jinka a zuciyata ina burin muyi doguwar rayuwa daita ki daina damun kanki dan Allah ."
Abinda ke tayarwa mumy hankali bai wuce ramar da yaranta guda suka yi ba badamasi da muradi ,ramarsu ta fito fili sosai da an kallesu an san suna cikin tsanani damuwa , ta kalli badamasi dake zaune a gabanta "meke damunka "? "Idan ciwon matarka ne yasa ka damu kanka wannan ai lalura ce kayi fatan Allah ya bata lafiya tunda mumy ta soma magana yayi shiru ya kasa cewa "uffan saboda shi kadai yasan abinda ke damunsa neman wanda zai tattauna matsalar yake yana son afra tamkar ransa Amman bazai iya jurar tana kwakwan son waninsa ba ,yanzu damuwarta tayi yawa ta kara lalacewa daga kuka sai kuka gaba-daya ta zauce a hankali ya mike cike da sanyi jiki ya fita ..
Ya badmasi na fita ta fito ta nufi dakinsu muradi sabon tashi hankali ta iske dan kuwa hawaye ta gani yana zubowa daga Idanunshi gaba-daya ta rude itama ta kama kuka tana tambayarsa dalilin kuka cikin sanyi murya yace "kwantar da hankalinki mumy babu abinda ke damuna kukan dadi ne "kukan dade ? mumy ta tambayesa tana riko hannunsa "eh ya girgiza mata kai " ban taba tunanin anan duniya rayuwata zata dawo haka ba mumy ,kin min komai a rayuwa wadan nan hawayen dake zuba na tsantsar kaunarki ne mumy da farinciki kasancewata a karkashinki gashi kuma zaku mallaka min abinda zuciyata ke so mumy ta dinga masa addu'a Allah ya sanya alkhairi a rayuwar aurenka muradi jikinsa yayi sanyi yana fatan auren ya zamo alkhairi a gareshi yana jin zafin yadda kisna ke nuna tsanarsa ƙarara da muzanta mahaifiyarsa da kalmar daya fi tsana a rayuwarsa ,shi fa har lokacin bai yarda mahaifiyarsa tayi ridda ba har ta koma ga Allah kullum cikin kyakkyawan zato yake mata "...
"Musa alkwarin zuciyata ne ,bani ba wani namiji sai Musa anan duniya bazan iya karya wannan alkawarin dake tsakaninmu ba gara ku barni haka babu aure dan wannan auren daidai yake da rasa rayuka , duk tsawon lokaci zan jira naga aurena da Musa jikina na bani zamuyi aure dashi bazan taba karyawa zuciyata alkwarin dana yi mata bazan cutar daita ba in hadata da wanda bai dace daita ba , bazan so wannan auren ba har abada dan Musa kadai zuciyata take so take muradi "wadan nan sune kalaman da kisna tayita maimaitawa a gaban iyayenta mumy da dady tana kuka kamar ranta zai fita Take mumy ta rufeta da fada bayan mumy ta gama fadanta tayi shiru kisna ta cigaba da bayyana musu sirrin zuciyarta akan Musa da alkwarin datayi masa ta basu hakuri akan suyi hakuri su hakura su barta ta auresa dan bazata iya bawa wani namiji kanta ba , da gari ya waye wanda yayi sauran kwana biyu a daura mata aure da muradi ta samu dady a dakinsa hawaye shabe shabe akan fuskarta ya mike zaune "uhmmmm yau kuma dame kika zo Sarkin marasa kunya kuka take sosai har ta taɓa zuciyarsa "ku aura mun Musa dan darajan Allah wallahi kamar yadda mumy ta fada Ni din sauransa ce babu abinda wani namiji zai samu gareni baya ga sauransa ta karasa maganar tana rufe idanunta da tafukan hannunta hawaye na siyaya "kiyi hakuri kisna ki lallashi zuciyarki ki amince da auren Aliyu shi bazai damu da komai naki ba ,nasani kina son musa nasani da haka amman ina jin ciwon tarrayarki dashi saboda ba yaron kirki bane yana sonki ne saboda wani manufa kuma ya samu tun da gashi kin fada da bakinki amman duk da haka bana sonki dashi , duk qaunar da kike masa kiyi hakuri da sauyin da Allah yayi miki dan wallahi ko haihuwa kika yi dashi karewar kanki da kika bashi bazan taba sonshi ba kuma bazan yi farinciki ba zan dangwama cikin bakinciki .
ta share hawayenta "kayi hakuri dady wallahi Musa bashi da wani abu dan Allah kada ku aurar dani ga wani ku kyaleni dashi dady ya jima yana kallonta daga bisani yaja dogon numfashi "kisna kice kika fi cancanta kiyi hakuri bamu ba ki auri zabinmu bazan yi hakuri na aura miki wannan yaron ba aurensa fitina ce gaba-daya gareni "dan iskan yaro mayaudari ba wai kaji dady kisna har kudi ta dauka tabawa yaron nan ya siya mota gashi can sai famtamawa yake da mata a gari ya barta da wahala inji cewar Samir madu yace bar wahalliya banza ni wallahi dasu dady zasu iya da sun hakura ta auri shegen yaron nan " Samir yace ",illar abun dai ko ta auresa sai ta dawo ni ba boka ba ni ba malam ba amman nasan sai ta dawo kuma lokacin da zata dawo din karshenta da zuri'a a tsakanisu haka za'a zo abashi hakuri ace ya amsheta "wannan kuma haka ne inji cewar dady ,kisna ta mike tana kuka "duk wanda ya sake cewa da musa mayaudari ne ban yafe masa ba ta nufi kofar fita a fusace Samir ya fito daga dakin ya damkota tare da daga hannu zai kwada mata mari daga bayansa yaji an rike masa hannu kada ka mareta rabu daita me ma tayi maka?"
Muna saida ingantattun maganin mata masu kyau da nagarta wanda ko da kudinka sai da rabonka tsimi , zumar Mata, gunba, gari insertion,kaza,zakara ,
jigida dadai sauransu.
1.Tsumi Yana saukarwa mace niima Kuma bazataji wuyar jimai ba.
2. Zuma Tana taimakawa wurin Jin sha'awa Kuma itama Tana taimakawa wurin jindadin jima'i.
3.insertion( Dan matsi) daban dabanne akwai Wanda ke matse mace kuma yake saukar da ruwan ni'ima sannan akwai na mallaka , idan ana bukata a tuntubi wannan number
234 815 945 0159..
addu'ar Sudais
[7/19, 5:32 PM] +234 803 631 5951: 💗💗💗💗💗💗
CUTAR DA KAI
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Page 41
~TRUE LIFE STORY~
*PAID BOOK*
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
"Wannan littafin na kudi ne ,mai bukata karanta shi zai tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number alert +234 803 238 4602 domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne . "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi za'a iya tuntu'bar Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos lace da kamfala ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da chiganvy, volyal lace duk akan farashi mai sauki ,ga mai bukatar siyan ɗaya ko sari yayi magana ta wannan number 08059623096.
.....Take jikin musa ya ɗauki rawa sakamakon idanunsa da suka sauka akan muradi tsaye dan bazai taba manta irin wahalar daya sha a hannunsa ba ,a matukar gigice ya waigo ya kalli gefensa inda kisna ke tsaye tana kallon muradi ranta a matukar bace dan ba tayi tsammani shi dady zai turo mata ba a matsayin wanda zai ɗauketa ta dauka direba zai turo mata kamar yadda sukayi dashi a waya ,su sauke musa a unguwarsu su kuma su k'arasa gida wayar hannunta data dauki karar yasa hankalin musa sake tashi dan yasan duk yadda akayi kiran daga mutumin daya fi jin tsoron haduwa da shi ne fiyye da kowani halitta a duniya , ita kuwa kisna ko ajikinta babu wani alamar tsoro a tattare daita illa cigaba da kallon muradi take yana kokarin nemanta har lokacin kamalarsa da tsananin kyawunsa na nan ya sake fita dabam acikin mutane sai dai ita duk wannan nagartartashi basa burgeta bare su d'ad'ata da kasa ."
cikin tsananin tsoro musa yayi kasa da muryarsa sosai ta yadda daga shi sai ita zasu iya ji sannan ya soma magana "yanzu ya zamu yi kenan ifemi ? " ya kamata na bar gurin nan tun kafin ya ganmu mu hadu da ɓacin rai gashi banason na haifar miki da damuwa daga dawowarki . "karka damu babu abinda zai faru sai alkhairi da da yanzu dabam , yanzu fa sheakaruna shatakwas a duniya nasan abinda nake yi ,kuma nasan abinda ke damuna , ina da yancin kaina ina da damar da zan zabarwa kaina wanda zanyi rayuwa dashi dan haka ka natsu ka kwantar da hankalinka babu abinda zai faru ta wannan da kake gani mai sauki ne zo muje ifemi karka zama matsoraci mana "ta k'arasa maganar tana daukar wayarta dake kara ta manna a kunneta " na ganka gani nan " ta fada a takaice tare da katse kiran batare da ta bari yayi magana ba "ifemi janyo wannan akwatin idan mun sauke ka dashi zaka wuce gida dan tsarabanka ne a ciki , zuciyar musa ta cika da tsananin mamaki mara misaltuwa ya rasa wani irin so kisna take masa "da me ya kamata ya biyata wannan tarin soyayyar da take masa ?" ya tambayi kanshi yana sanyawa jikinsa kuzarin biyota sai da suka kusan karaasowa daf da muradi sannan ya lura da kisna ce ke tahowa tare da Musa take qirjinsa yayi wani mahaukacin bugawa da karfi yana matukar mamakin ganinsu a tare a daidai lokacin , idanunsa ya musisika domin tabbatar da su din yake gani ko kuwa gizo suke masa ? koda ya sake kallonsu ya tabbatarwa kansa tabbas su din ne suke kokarin karasowa inda yake zuciyarsa ce gaba-daya ta tsaya ta daina aiki na wuncin gadi kafin daga baya ta soma bugawa da matsanancin karfin gaske "wannan wacce irin zazzafar soyayya ce ta afkawa rayuwar kisna "? "Kenan duk nisan da tayi da kasar suna tare ne ? ya tambayi zuciyarsa tare da sauke wani wahalallen numfashi yana gyara tsayuwarsa a daidai lokacin da suka wuce ta gabansa ko kallon inda yake tsaye kisna bata yi ba ta karasa bayan mota tana kokarin bude boot zata saka kayan a zuciye muradi ya kasaso inda suke "me wannan yake yi tare dake ? "Kice min mafarki ne bashi bane tare dake ? " a hankali ta d'ago idanunta tayi masa kallon banza sannan tace "I don't understand you what are you try to say ? "shiru yayi ya kasa cewa komai dan kwakwaran motsi ma kasawa yayi ya zuba mata ido yana dubanta har ta sa akwatin ta bawa musa umarni saka na hannunsa ta rufe boot ta nufi murfin mota zata budewa musa muradi ya karaso ya rike hannunta "bazan bari wannan katantawar ya shigar min mota ba kisa mutuncina ya zube " fixge hannunta tayi a fusace tana daga masa hannunsa "sai me idan bai shiga ba ? "Tayi maganar tana masa kallon sama da kasa a wulakance sai lokacin muradi ya tabbata da gaskiyar da yake nema tabbas dai ba mafarki bane musa da gaske a gefenta "ya Salam ...." ya furta yana furzar da iska hankalinsa idan yayi dubu to ya gama tashi ...
a hankali Musa ya karaso kusa daita ya marairaice fuska da murya kamar zai mata kuka "ifemi kiyi hakuri ki bishi ke daya ni zan samu mota na koma gida , banason ki shiga damuwa a sanadiyyana plz do what I said before everything could have miss up to us kallonsa muradi yayi duk da tsananin bakinciki da takaicin da yake ciki "bana fatan wani abu ya sameki ,"kalli yadda surar jikinki ta koma ? muradi ya dubeta sosai fatar jikinta tayi luwai luwai ta maseefar canzawa tamkar tana wanka da madara sai sheki take zubawa " bazan so a taba min lafiyar jikinkinki ba ki taimakeni ki shiga kinji ifemi babu mutsu bare gardama ta shiga bayan mota ta zauna ya maida murfin kofar ya rufe , sannan ya dawo ya bude Boot ya fito da jakar kayansa ya soma ja take masu texi dake paturo a gurin suka yo kansa ya mikawa daya daga cikinsu jakar ya shiga bayan mota shima direban ya saka jakar a bayan motar ya shiga suka wuce ..."
Muradi ya furzar da iska mai zafi yana takaicin hali irin na kisna na rashin kamun kai yarinya sai taurin kan bala'in kamar na mutanen farko shi dai this time a round babu ruwansa ya yi iyakacin kokarinsa akanta bashi da wani sauran dabara tunda duk bata ga kokarinsu na son inganta rayuwarta ba, hasalima musa bashi da laifi kamar yadda zee ta Sha fada itace mai laifi dan data hakura dashi tabbas zai hakura daita ya cigaba da rayuwarsa tunda yasan ba ajinsa bace naunauyen ajiyar zuciya ya sauke sannan yayi kokarin sanyawa jikinsa jarumta ya bude bangaren da take zaune muryarsa a dake yace "ki fito ki koma gaba ki zauna dan nan babu direbanki "tayi masa banza tamkar ba mutun ke mata magana ba shima kallonta ya tsaya yana yi ta bala'in hade fuska tare da kamewa guri daya tana cizan lip's dinta na kasa ganin bata da niyyar fitowa ya danko tsintsiyar hannunta "you very stupid fito ki koma gaba cikin bakincikinta ya fito daita ya bude gaban motar ya shigar daita ya rufe ya zagaya kafin tayi yunkurin fitowa ya shiga ya rufe ko'ina na motar sannan ya figeta da gudu ...."
Tashin motar da gudu yayi daidai da tarwatsewar zuciyarta ,kanta ya sara da matsanancin karfi saboda yadda yaja motar ,a hankali ta kalli gefen da yake zaune fuskarta cike da maseefa da niyyar sauke masa abinda ke kanshi yayi daidai da shima ya waigo idanunsu suka tsarke cikin juna a tare zukatansu ya buga a dalilin yanayin fuskokinsu ko wannensu fuska a daure ,duk da yaso dauke kwayar Idanunshi akanta amman ya kasa kisna tayi masa kwarji ga wani kyau na musamman da fuskarta ke dauke dashi ta dawo tamkar wata buturiyar Ingila gabad'aya jikinsa yayi bala'in sanyi daga kallon tsanar da take masa,shima take yaji kasalar tsanarta ta sauko masa ta mamaye ilahirin jikinsa abinda bai taba ji ba kenan a iya tsawon rayuwarsa yasan dai baya tsanarta haka zalika baya sonta komai yana yi mata ne darajan iyayenta da bai san da abinda zai saka musu dashi ba .
itace ta fara janye idanunta ta maidashi gefen titi yayinda shi kuma ya cigaba da kallonta saurin kallon gabansa yayi a dalilin hon din da wani mai mota jep yayi masa hade da ihu muradi yayi saurin juya kan stearing motar ya kaucewa motar gabad'aya kisna ta zubo jikinsa tana kwalla wani razannaniyar kara cikin tsananin tsoro, ya tsaida motar zuciyarsa na wani irin dokawa da matsanancin karfi , mutumin dake da jep ya tsaya yana masa magana cikin zafin rai muradi yayi warning din glass yana bashi hakuri dan yasan kuskurensa ne dana makirar dake zaune a gefensa tsaki ya ja yana kallonta makale ajikinta "makira yarinyar kawai ga tsoro ga ban tsoro wallahi baba mai gadi ya baki sunan daya dace dake yayi maganar a cikin zuciyarsa , a hankali sihirtaccen kamshin turarenta mai sanyi yayiwa zuciyarsa diran bazata ya runtse idanunsa gam yana sauke zazzafan ajiyar zuciya tare da jin haushin kansa da bai yakiceta daga jikinsa ba yana ƙoƙarin janye jikinsa tayi saurin janye jikinta daga nashi cikin jin haushin haduwar da jikinsu yayi tana jan dogon tsaki tare da dafe kanta "wash ya dai kamata ka maida hankalinka akan abinda kake yi dan rayuwata nada matukar muhimmancin gareni ta karasa maganar tan a sake jan wani tsaki lokacin da taji kanta ya sara fiyye da ka'ida domin kuwa wani irin sara yake mata kamar ana sassara mata guduma , lumshe idanuwanta tayi sannan tayi baya da kujerar da take zaune ta kwantar da kanta saman kujerar tana sauke numfashi a hankali tsaki yaja mata fiyye da wanda tayi sannan yaja motar suka hau kan titi .."
Har suka iso gida bata sani ba sai da taji yana waya da Samir "Samir ai mun iso gida yanzu zan taho plz ka bani wasu yan mintuna " ta bude idanunta ta yunkura ta fito daga cikin motar ko ta kan akwatin kayanta bata bi ba haka zalika bata kalli inda yake ba illa muryarta da yaji yo a lokacin da yake kokarin fitowa daga cikin motar "ka karasa aikinka ka shigo min da akwatina dan baka da maraba da dan aikin gidan nan "tana gama fadar haka ta soma tafiya a natse shima bai ce mata uffan ba dan bashi lokacinta ya raina duk wani ajinta da isa tunda zata iya makalewa mutun kamar musa ya fito ya bawa sabon direbansu lawan umarnin ya jingina jikinsa da mota yana kallon yadda take rausaya har ta kusa kai cikin parlour'n gidansu tana shiga ta hango mumy ta saki kara tare da kwalla mata kira ta karasa da gudu ta rungumeta tsam tana dariyar murna gefe guda kuma zuciyarta na cike da tsoro duk da tasan da wuya muradi ya fadi ya ganta tare da musa mumy ta zareta a jikinta tana kallonta kawai saboda ganin yadda ta kara girma da kyau ta